< Ezekiyel 20 >

1 A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
And it came to pass in the seventh year, in the fifth month, the tenth day of the month, that certain of the elders of Israel came to inquire of the LORD, and sat before me.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the LORD came unto me, saying:
3 “Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
'Son of man, speak unto the elders of Israel, and say unto them: Thus saith the Lord GOD: Are ye come to inquire of Me? As I live, saith the Lord GOD, I will not be inquired of by you.
4 “Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
Wilt thou judge them, son of man, wilt thou judge them? cause them to know the abominations of their fathers;
5 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
and say unto them: Thus saith the Lord GOD: In the day when I chose Israel, and lifted up My hand unto the seed of the house of Jacob, and made Myself known unto them in the land of Egypt, when I lifted up My hand unto them, saying: I am the LORD your God;
6 A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
in that day I lifted up My hand unto them, to bring them forth out of the land of Egypt into a land that I had sought out for them, flowing with milk and honey, which is the beauty of all lands;
7 Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
and I said unto them: Cast ye away every man the detestable things of his eyes, and defile not yourselves with the idols of Egypt; I am the LORD your God.
8 “‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
But they rebelled against Me, and would not hearken unto Me; they did not every man cast away the detestable things of their eyes, neither did they forsake the idols of Egypt; then I said I would pour out My fury upon them, to spend My anger upon them in the midst of the land of Egypt.
9 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
But I wrought for My name's sake, that it should not be profaned in the sight of the nations, among whom they were, in whose sight I made Myself known unto them, so as to bring them forth out of the land of Egypt.
10 Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
So I caused them to go forth out of the land of Egypt, and brought them into the wilderness.
11 Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
And I gave them My statutes, and taught them Mine ordinances, which if a man do, he shall live by them.
12 Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
Moreover also I gave them My sabbaths, to be a sign between Me and them, that they might know that I am the LORD that sanctify them.
13 “‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
But the house of Israel rebelled against Me in the wilderness; they walked not in My statutes, and they rejected Mine ordinances, which if a man do, he shall live by them, and My sabbaths they greatly profaned; then I said I would pour out My fury upon them in the wilderness, to consume them.
14 Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
But I wrought for My name's sake, that it should not be profaned in the sight of the nations, in whose sight I brought them out.
15 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
Yet also I lifted up My hand unto them in the wilderness, that I would not bring them into the land which I had given them, flowing with milk and honey, which is the beauty of all lands;
16 domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
because they rejected Mine ordinances, and walked not in My statutes, and profaned My sabbaths — for their heart went after their idols.
17 Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
Nevertheless Mine eye spared them from destroying them, neither did I make a full end of them in the wilderness.
18 Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
And I said unto their children in the wilderness: Walk ye not in the statutes of your fathers, neither observe their ordinances, nor defile yourselves with their idols;
19 Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
I am the LORD your God; walk in My statutes, and keep Mine ordinances, and do them;
20 Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
and hallow My sabbaths, and they shall be a sign between Me and you, that ye may know that I am the LORD your God.
21 “‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
But the children rebelled against Me; they walked not in My statutes, neither kept Mine ordinances to do them, which if a man do, he shall live by them; they profaned My sabbaths; then I said I would pour out My fury upon them, to spend My anger upon them in the wilderness.
22 Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
Nevertheless I withdrew My hand, and wrought for My name's sake, that it should not be profaned in the sight of the nations, in whose sight I brought them forth.
23 Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
I lifted up My hand unto them also in the wilderness, that I would scatter them among the nations, and disperse them through the countries;
24 domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
because they had not executed Mine ordinances, but had rejected My statutes, and had profaned My sabbaths, and their eyes were after their fathers' idols.
25 Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
Wherefore I gave them also statutes that were not good, and ordinances whereby they should not live;
26 na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
and I polluted them in their own gifts, in that they set apart all that openeth the womb, that I might destroy them, to the end that they might know that I am the LORD.
27 “Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
Therefore, son of man, speak unto the house of Israel, and say unto them: Thus saith the Lord GOD: In this moreover have your fathers blasphemed Me, in that they dealt treacherously with Me.
28 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
For when I had brought them into the land, which I lifted up My hand to give unto them, then they saw every high hill, and every thick tree, and they offered there their sacrifices, and there they presented the provocation of their offering, there also they made their sweet savour, and there they poured out their drink-offerings.
29 Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
Then I said unto them: What meaneth the high place whereunto ye go? So the name thereof is called Bamah unto this day.
30 “Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
Wherefore say unto the house of Israel: Thus saith the Lord GOD: When ye pollute yourselves after the manner of your fathers, and go after their abominations,
31 Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
and when, in offering your gifts, in making your sons to pass through the fire, ye pollute yourselves with all your idols, unto this day; shall I then be inquired of by you, O house of Israel? As I live, saith the Lord GOD, I will not be inquired of by you;
32 “‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
and that which cometh into your mind shall not be at all; in that ye say: We will be as the nations, as the families of the countries, to serve wood and stone.
33 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
As I live, saith the Lord GOD, surely with a mighty hand, and with an outstretched arm, and with fury poured out, will I be king over you;
34 Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
and I will bring you out from the peoples, and will gather you out of the countries wherein ye are scattered, with a mighty hand, and with an outstretched arm, and with fury poured out;
35 Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
and I will bring you into the wilderness of the peoples, and there will I plead with you face to face.
36 Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Like as I pleaded with your fathers in the wilderness of the land of Egypt, so will I plead with you, saith the Lord GOD.
37 Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
And I will cause you to pass under the rod, and I will bring you into the bond of the covenant;
38 Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
and I will purge out from among you the rebels, and them that transgress against Me; I will bring them forth out of the land where they sojourn, but they shall not enter into the land of Israel; and ye shall know that I am the LORD.
39 “‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
As for you, O house of Israel, thus saith the Lord GOD: Go ye, serve every one his idols, even because ye will not hearken unto Me; but My holy name shall ye no more profane with your gifts, and with your idols.
40 Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
For in My holy mountain, in the mountain of the height of Israel, saith the Lord GOD, there shall all the house of Israel, all of them, serve Me in the land; there will I accept them, and there will I require your heave-offerings, and the first of your gifts, with all your holy things.
41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
With your sweet savour will I accept you, when I bring you out from the peoples, and gather you out of the countries wherein ye have been scattered; and I will be sanctified in you in the sight of the nations.
42 Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
And ye shall know that I am the LORD, when I shall bring you into the land of Israel, into the country which I lifted up My hand to give unto your fathers.
43 A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
And there shall ye remember your ways, and all your doings, wherein ye have polluted yourselves; and ye shall loathe yourselves in your own sight for all your evils that ye have committed.
44 Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
And ye shall know that I am the LORD, when I have wrought with you for My name's sake, not according to your evil ways, nor according to your corrupt doings, O ye house of Israel, saith the Lord GOD.'
45 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the LORD came unto me, saying:
46 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
'Son of man, set thy face toward the South, and preach toward the South, and prophesy against the forest of the field in the South;
47 Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
and say to the forest of the South: Hear the word of the LORD: Thus saith the Lord GOD: Behold, I will kindle a fire in thee, and it shall devour every green tree in thee, and every dry tree, it shall not be quenched, even a flaming flame; and all faces from the south to the north shall be seared thereby.
48 Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
And all flesh shall see that I the LORD have kindled it; it shall not be quenched.'
49 Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”
Then said I: 'Ah Lord GOD! they say of me: Is he not a maker of parables?'

< Ezekiyel 20 >