< Ezekiyel 2 >
1 Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”
Ele me disse: “Filho do homem, fique de pé, e eu falarei com você”.
2 Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.
O Espírito entrou em mim quando falou comigo, e me pôs em pé; e eu ouvi aquele que falou comigo.
3 Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.
Ele me disse: “Filho do homem, eu te envio aos filhos de Israel, a uma nação de rebeldes que se rebelaram contra mim”. Eles e seus pais transgrediram contra mim até os dias atuais.
4 Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’
As crianças são impudentes e duras de coração. Eu os envio a eles e vocês lhes dirão: 'Isto é o que o Senhor Javé diz'.
5 Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.
Eles, quer ouçam, quer se recusem - por serem uma casa rebelde - saberão que houve um profeta entre eles.
6 Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.
Tu, filho do homem, não tenhas medo deles, nem tenhas medo das suas palavras, embora briers e thorns estejam contigo, e habites entre escorpiões. Não tenha medo de suas palavras, nem se assuste com sua aparência, apesar de serem uma casa rebelde.
7 Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su’yan tawaye ne.
Dir-lhes-eis minhas palavras, quer ouçam quer recusem, pois eles são os mais rebeldes.
8 Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”
Mas você, filho do homem, ouça o que eu lhe digo. Não seja rebelde como aquela casa rebelde. Abra sua boca, e coma o que eu lhe dou”.
9 Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,
Quando olhei, eis que uma mão estava estendida para mim; e eis que um pergaminho de um livro estava nele.
10 wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.
Ele o espalhou diante de mim. Estava escrito dentro e fora; e nele estavam escritas lamentações, luto e infortúnios.