< Ezekiyel 2 >
1 Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”
Wathi kimi, “Ndodana yomuntu, sukuma ume ngezinyawo zakho ngikhulume lawe.”
2 Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.
Esakhuluma uMoya wafika kimi wangimisa ngezinyawo zami, ngamuzwa esekhuluma lami.
3 Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.
Wathi, “Ndodana yomuntu, ngiyakuthuma kuma-Israyeli, isizwe esihlamukayo esangihlamukelayo, laboyise bangihlamukela kuze kube yilolusuku.
4 Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’
Abantu engikuthuma kubo balenkani njalo bayiziqholo. Wothi kubo, ‘Nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi.’
5 Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.
Njalo langabe bayalalela loba bangalaleli ngoba bayindlu ehlamukayo, bazakwazi ukuthi umphrofethi ubekhona phakathi kwabo.
6 Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.
Njalo wena ndodana yomuntu, ungabesabi kumbe wesabe amazwi abo. Ungesabi lanxa usuhonqolozelwe ngameva njalo usuhlala phakathi kwabofezeya. Ungakwesabi lokho abakutshoyo loba uthuthunyeliswe yibo, lanxa beyindlu ehlamukayo.
7 Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su’yan tawaye ne.
Kumele ukhulume amazwi ami kubo langabe bayalalela loba kabalaleli, ngoba bangabahlamuki.
8 Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”
Kodwa wena, ndodana yomuntu, lalela lokhu engikutshoyo kuwe. Ungahlamuki njengendlu leyana ehlamukayo; vula umlomo wakho udle lokhu engikupha khona.”
9 Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,
Ngakhangela ngabona isandla esaselulelwe kimi. Phakathi kwaso kwakulomqulu,
10 wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.
awutshombulula phambi kwami. Emaceleni awo womabili kwakubhalwe amazwi okukhala lokulila kanye losizi.