< Ezekiyel 2 >
1 Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”
This was the appearance of the likeness of the glory of the Lord. And I saw and fell upon my face, and heard the voice of one speaking: and he said to me, Son of man, stand upon your feet, and I will speak to you.
2 Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.
And the Spirit came upon me, and took me up, and raised me, and set me on my feet: and I heard him speaking to me.
3 Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.
And he said to me, Son of Man, I send you forth to the house of Israel, them that provoke me; who have provoked me, they and their fathers to this day.
4 Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’
And you shall say to them, Thus says the Lord.
5 Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.
Whether then indeed they shall hear or fear, (for it is a provoking house, ) yet they shall know that you are a prophet in the midst of them.
6 Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.
And you, son of man, fear them not, nor be dismayed at their face; (for they will madden and will rise up against you round about, and you dwell in the midst of scorpions): be not afraid of their words, nor be dismayed at their countenance, for it is a provoking house.
7 Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su’yan tawaye ne.
And you shall speak my words to them, whether they will hear or fear: for it is a provoking house.
8 Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”
And you, son of man, hear him that speaks to you; be not you provoking, as the provoking house: open your mouth, and eat what I give you.
9 Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,
And I looked, and behold, a hand stretched out to me, and in it a volume of a book.
10 wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.
And he unrolled it before me: and in it the front and the back were written [upon]: and there was written [in it] Lamentation, and mournful song, and woe.