< Ezekiyel 19 >
1 “Ka yi makoki game da sarakunan Isra’ila
“Qhinqani isililo ngamakhosana ako-Israyeli
2 ka ce, “‘Mahaifiyarki zakanya ce cikin zakoki! Takan kwanta cikin’yan zakoki ta kuma yi renon kwiyakwiyanta.
lithi: ‘Yeka isilwanekazi esasingunyoko phakathi kwezilwane! Salala phansi phakathi kwezilwane ezisakhulayo sondla imidlwane yaso.
3 Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta, ya yi girma ya zama zaki mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Sakhulisa omunye wemidlwane yaso waba yisilwane esilamandla wafunda ukudabula okubanjelwe ukudliwa, wadla labantu.
4 Al’ummai suka ji labarinsa, aka kuma kama shi cikin raminsu. Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.
Izizwe zezwa ngawo wasuthiywa egodini lazo. Zawuhola ngezingwegwe zawusa elizweni laseGibhithe.
5 “‘Sa’ad da ta ga sa zuciyarta bai cika ba, abin da take fata gani ya tafi, sai ta ɗauki wani daga cikin kwiyakwiyanta ta mai da shi zaki mai ƙarfi.
Kwathi sibona ithemba laso lingagcwalisekanga, ithemba laso lingasekho, sathatha omunye wemidlwane yaso sawenza waba yisilwane esilamandla.
6 Ya yi ta yawo a cikin zakoki, gama yanzu shi zaki ne mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Wanyonyoba phakathi kwezilwane ngoba wawuyisilwane esilamandla. Wafunda ukudabula okubanjelwe ukudliwa, wadla labantu.
7 Ya rurrushe kagaransu ya kuma ragargaza biranensu. Ƙasar da dukan waɗanda suke cikinta sun tsorata da jin rurinsa.
Wadiliza izinqaba zabo wachitha lamadolobho abo. Ilizwe kanye labo bonke ababekulo bathuthumeliswa yikubhonga kwawo.
8 Sai al’ummai suka tayar masa, waɗannan daga yankunan da suke kewaye. Suka yafa raga dominsa ya kuwa fāɗa cikin raminsu.
Izizwe zawuvukela, zivela ezindaweni eziwuzingelezileyo. Zendlala amambule azo phezu kwawo wawela egodini labo.
9 Da ƙugiyoyi suka ja shi cikin keji suka kawo shi wurin sarkin Babilon. Suka sa shi cikin kurkuku, saboda haka ba a ƙara jin rurinsa a kan duwatsun Isra’ila ba.
Bawudonsela ekhejini ngezingwegwe bawusa enkosini yaseBhabhiloni. Bawufaka entolongweni, ngakho ukubhonga kwawo akuzwakalanga futhi ezintabeni zako-Israyeli.
10 “‘Mahaifiyarku kamar kuringa ce a cikin gonar inabi da aka shuka kusa da ruwa; ta ba da’ya’ya da kuma cikakkun rassa saboda yalwan ruwa.
Unyoko wayenjengevini elihlanyelwe ngasemanzini esivinini sakho; sasithela izithelo njalo silezingatsha ezinengi ngenxa yamanzi amanengi.
11 Rassanta suka yi ƙarfi, suka dace da sandar mai mulki. Ta yi tsayi zuwa sama ana ganin ta saboda tsayinta da kuma saboda yawan rassanta.
Ingatsha zaso zaziqinile zifanele intonga yombusi. Sasiphakeme siphezulu le ngaphezu kwamahlamvu aminyeneyo, sibonakala ngobude baso langezingatsha zaso ezinengi.
12 Amma aka tumɓuke ta cikin fushi aka jefar da ita a ƙasa. Iskar gabas ta sa ta yanƙwane, aka kakkaɓe’ya’yanta; rassanta masu ƙarfi suka bushe wuta kuma ta cinye su.
Kodwa sasitshunwa ngokuthukuthela saphoselwa phansi. Umoya wasempumalanga wasomisa, izithelo zaso zaqhululwa; ingatsha zaso eziqinileyo zabuna umlilo wazitshisa.
13 Yanzu an shuka ta a hamada, a busasshiyar ƙasa marar ruwa.
Khathesi sesihlanyelwe enkangala, elizweni elitshisayo lelomileyo.
14 Wuta ta fito daga jikin rassanta ta cinye’ya’yanta. Babu sauran reshe mai ƙarfin da ya rage a kanta da ya dace da sandar mai mulki.’ Wannan waƙa ce kuma za a yi amfani da ita a matsayin makoki.”
Umlilo umemetheke usuka kolunye lwezingatsha ezinkulu, watshisa izithelo zaso. Akulagatsha oluqinileyo oluseleyo kuso olufanele intonga yombusi.’ Lesi yisililo njalo sizasetshenziswa njengesililo.”