< Ezekiyel 19 >

1 “Ka yi makoki game da sarakunan Isra’ila
Et toi, prophète, emploie un chant lugubre pour les princes d’Israël,
2 ka ce, “‘Mahaifiyarki zakanya ce cikin zakoki! Takan kwanta cikin’yan zakoki ta kuma yi renon kwiyakwiyanta.
Et tu diras: Pourquoi ta mère, qui est une lionne, s’est elle reposée parmi des lions, et a-t-elie nourri ses petits au milieu des lionceaux?
3 Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta, ya yi girma ya zama zaki mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Elle a fait sortir un de ses lionceaux, et il est devenu lion; et il a appris à ravir sa proie et à dévorer des hommes.
4 Al’ummai suka ji labarinsa, aka kuma kama shi cikin raminsu. Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.
Et les peuples ont ouï parler de lui, et ils l’ont saisi, mais non sans recevoir des blessures, et ils l’ont emmené enchaîné en Egypte.
5 “‘Sa’ad da ta ga sa zuciyarta bai cika ba, abin da take fata gani ya tafi, sai ta ɗauki wani daga cikin kwiyakwiyanta ta mai da shi zaki mai ƙarfi.
Comme la mère vit qu’elle était sans force, et que son attente était détruite, elle prit un autre de ses lionceaux, l’établit lion.
6 Ya yi ta yawo a cikin zakoki, gama yanzu shi zaki ne mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Il marchait parmi les lions, et il devint lion; et il apprit à ravir sa proie et à dévorer des hommes.
7 Ya rurrushe kagaransu ya kuma ragargaza biranensu. Ƙasar da dukan waɗanda suke cikinta sun tsorata da jin rurinsa.
Il apprit à faire des veuves et à réduire les cités en déserts: et la terre ainsi que sa plénitude fut désolée à la voix de son rugissement.
8 Sai al’ummai suka tayar masa, waɗannan daga yankunan da suke kewaye. Suka yafa raga dominsa ya kuwa fāɗa cikin raminsu.
Et contre lui des nations s’assemblèrent de toutes parts des provinces, et elles étendirent sur lui leurs rets, il fut pris, mais eu leur faisant des blessures.
9 Da ƙugiyoyi suka ja shi cikin keji suka kawo shi wurin sarkin Babilon. Suka sa shi cikin kurkuku, saboda haka ba a ƙara jin rurinsa a kan duwatsun Isra’ila ba.
Et ils le mirent dans une cage, l’emmenèrent enchaîné au roi de Babylone; et ils le mirent dans la prison, afin qu’on n’entendit plus sa voix sur les montagnes d’Israël.
10 “‘Mahaifiyarku kamar kuringa ce a cikin gonar inabi da aka shuka kusa da ruwa; ta ba da’ya’ya da kuma cikakkun rassa saboda yalwan ruwa.
Ta mère comme la vigne a été plantée dans ton sang sur le bord de l’eau; son fruit et ses feuilles ont crû par de grandes eaux.
11 Rassanta suka yi ƙarfi, suka dace da sandar mai mulki. Ta yi tsayi zuwa sama ana ganin ta saboda tsayinta da kuma saboda yawan rassanta.
Et ses branches solides sont devenues des sceptres de dominateurs, et sa tige s’est élevée parmi ses feuilles, et elle a vu sa hauteur parmi la multitude de ses sarments.
12 Amma aka tumɓuke ta cikin fushi aka jefar da ita a ƙasa. Iskar gabas ta sa ta yanƙwane, aka kakkaɓe’ya’yanta; rassanta masu ƙarfi suka bushe wuta kuma ta cinye su.
Et elle a été arrachée avec colère, et jetée sur la terre; et un vent brûlant a desséché son fruit; les branches qui faisaient sa force se sont flétries et devenues arides; un feu l’a dévorée.
13 Yanzu an shuka ta a hamada, a busasshiyar ƙasa marar ruwa.
Et maintenant elle a été transplantée dans le désert, dans une terre sans voie et altérée.
14 Wuta ta fito daga jikin rassanta ta cinye’ya’yanta. Babu sauran reshe mai ƙarfin da ya rage a kanta da ya dace da sandar mai mulki.’ Wannan waƙa ce kuma za a yi amfani da ita a matsayin makoki.”
Et il est sorti un feu de la tige de ses rameaux, lequel a dévoré son fruit, et il n’y a plus eu en elle une tige forte, sceptre de dominateurs. C’est un chant lugubre, et ce sera un chant lugubre.

< Ezekiyel 19 >