< Ezekiyel 19 >
1 “Ka yi makoki game da sarakunan Isra’ila
Et toi, prononce une complainte sur les princes d’Israël,
2 ka ce, “‘Mahaifiyarki zakanya ce cikin zakoki! Takan kwanta cikin’yan zakoki ta kuma yi renon kwiyakwiyanta.
et dis: Ta mère, qu’était-ce? Une lionne. Elle était couchée parmi les lions; C’est au milieu des lionceaux Qu’elle a élevé ses petits.
3 Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta, ya yi girma ya zama zaki mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Elle éleva l’un de ses petits, Qui devint un jeune lion, Et qui apprit à déchirer sa proie; Il dévora des hommes.
4 Al’ummai suka ji labarinsa, aka kuma kama shi cikin raminsu. Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.
Les nations entendirent parler de lui, Et il fut pris dans leur fosse; Elles mirent une boucle à ses narines et l’emmenèrent Dans le pays d’Égypte.
5 “‘Sa’ad da ta ga sa zuciyarta bai cika ba, abin da take fata gani ya tafi, sai ta ɗauki wani daga cikin kwiyakwiyanta ta mai da shi zaki mai ƙarfi.
Quand la lionne vit qu’elle attendait en vain, Qu’elle était trompée dans son espérance, Elle prit un autre de ses petits, Et en fit un jeune lion.
6 Ya yi ta yawo a cikin zakoki, gama yanzu shi zaki ne mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Il marcha parmi les lions, Il devint un jeune lion, Et il apprit à déchirer sa proie; Il dévora des hommes.
7 Ya rurrushe kagaransu ya kuma ragargaza biranensu. Ƙasar da dukan waɗanda suke cikinta sun tsorata da jin rurinsa.
Il força leurs palais, Et détruisit leurs villes; Le pays, tout ce qui s’y trouvait, fut ravagé, Au bruit de ses rugissements.
8 Sai al’ummai suka tayar masa, waɗannan daga yankunan da suke kewaye. Suka yafa raga dominsa ya kuwa fāɗa cikin raminsu.
Contre lui se rangèrent les nations D’alentour, des provinces; Elles tendirent sur lui leur rets, Et il fut pris dans leur fosse.
9 Da ƙugiyoyi suka ja shi cikin keji suka kawo shi wurin sarkin Babilon. Suka sa shi cikin kurkuku, saboda haka ba a ƙara jin rurinsa a kan duwatsun Isra’ila ba.
Elles mirent une boucle à ses narines, le placèrent dans une cage, Et l’emmenèrent auprès du roi de Babylone; Puis elles le conduisirent dans une forteresse, Afin qu’on n’entende plus sa voix sur les montagnes d’Israël.
10 “‘Mahaifiyarku kamar kuringa ce a cikin gonar inabi da aka shuka kusa da ruwa; ta ba da’ya’ya da kuma cikakkun rassa saboda yalwan ruwa.
Ta mère était, comme toi, semblable à une vigne, Plantée près des eaux. Elle était féconde et chargée de branches, A cause de l’abondance des eaux.
11 Rassanta suka yi ƙarfi, suka dace da sandar mai mulki. Ta yi tsayi zuwa sama ana ganin ta saboda tsayinta da kuma saboda yawan rassanta.
Elle avait de vigoureux rameaux pour des sceptres de souverains; Par son élévation elle dominait les branches touffues; Elle attirait les regards par sa hauteur, Et par la multitude de ses rameaux.
12 Amma aka tumɓuke ta cikin fushi aka jefar da ita a ƙasa. Iskar gabas ta sa ta yanƙwane, aka kakkaɓe’ya’yanta; rassanta masu ƙarfi suka bushe wuta kuma ta cinye su.
Mais elle a été arrachée avec fureur et jetée par terre; Le vent d’orient a desséché son fruit; Ses rameaux vigoureux ont été rompus et desséchés; Le feu les a dévorés.
13 Yanzu an shuka ta a hamada, a busasshiyar ƙasa marar ruwa.
Et maintenant elle est plantée dans le désert, Dans une terre sèche et aride.
14 Wuta ta fito daga jikin rassanta ta cinye’ya’yanta. Babu sauran reshe mai ƙarfin da ya rage a kanta da ya dace da sandar mai mulki.’ Wannan waƙa ce kuma za a yi amfani da ita a matsayin makoki.”
Le feu est sorti de ses branches, Et a dévoré son fruit; Elle n’a plus de rameau vigoureux Pour un sceptre de souverain. C’est là une complainte, et cela servira de complainte.