< Ezekiyel 19 >

1 “Ka yi makoki game da sarakunan Isra’ila
Et toi, chante une lamentation sur le prince d'Israël;
2 ka ce, “‘Mahaifiyarki zakanya ce cikin zakoki! Takan kwanta cikin’yan zakoki ta kuma yi renon kwiyakwiyanta.
Et dis: Pourquoi ma mère est-elle devenue une jeune lionne au milieu des lions? Pourquoi, au milieu des lions, a-t-elle multiplié ses lionceaux?
3 Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta, ya yi girma ya zama zaki mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Et un de ses lionceaux s'est élancé, et il est devenu lion, et il a appris à ravir sa proie, et il a dévoré des hommes.
4 Al’ummai suka ji labarinsa, aka kuma kama shi cikin raminsu. Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.
Et les nations en ont ouï parler, et il a été pris comme il les détruisait, et elles l'ont emmené, dans un filet, en la terre d'Égypte.
5 “‘Sa’ad da ta ga sa zuciyarta bai cika ba, abin da take fata gani ya tafi, sai ta ɗauki wani daga cikin kwiyakwiyanta ta mai da shi zaki mai ƙarfi.
Et la lionne, ayant vu qu'il était séparé d'elle, et que son espérance en lui avait péri, prit un autre de ses lionceaux, et le fit lion.
6 Ya yi ta yawo a cikin zakoki, gama yanzu shi zaki ne mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
Et celui-ci se montra au milieu des lions, et il devint lion, et il apprit à ravir sa proie, et il dévora des hommes.
7 Ya rurrushe kagaransu ya kuma ragargaza biranensu. Ƙasar da dukan waɗanda suke cikinta sun tsorata da jin rurinsa.
Et il se reput en son audace, et il dépeupla les villes de la voix de ses rugissements; et il désola la terre et ce qui la remplit.
8 Sai al’ummai suka tayar masa, waɗannan daga yankunan da suke kewaye. Suka yafa raga dominsa ya kuwa fāɗa cikin raminsu.
Et les peuples des royaumes l'entourèrent, et ils tendirent contre lui leurs filets, et pendant qu'il les détruisait il fut pris.
9 Da ƙugiyoyi suka ja shi cikin keji suka kawo shi wurin sarkin Babilon. Suka sa shi cikin kurkuku, saboda haka ba a ƙara jin rurinsa a kan duwatsun Isra’ila ba.
Et on le mit dans une cage de fer, enveloppé de son filet; et il arriva chez le roi de Babylone, qui le jeta en prison, afin qu'on n'entendit plus sa voix sur la montagne d'Israël.
10 “‘Mahaifiyarku kamar kuringa ce a cikin gonar inabi da aka shuka kusa da ruwa; ta ba da’ya’ya da kuma cikakkun rassa saboda yalwan ruwa.
Ta mère est comme une vigne et comme une fleur de grenadier planté au bord des eaux; son fruit et ses bourgeons ont crû dans l'abondance de l'eau.
11 Rassanta suka yi ƙarfi, suka dace da sandar mai mulki. Ta yi tsayi zuwa sama ana ganin ta saboda tsayinta da kuma saboda yawan rassanta.
Mais elle est devenue une verge pour la tribu des rois, et elle s'est élevée dans sa grandeur, au milieu des autres tiges. Et elle a vu sa grandeur en la multitude de ses rameaux.
12 Amma aka tumɓuke ta cikin fushi aka jefar da ita a ƙasa. Iskar gabas ta sa ta yanƙwane, aka kakkaɓe’ya’yanta; rassanta masu ƙarfi suka bushe wuta kuma ta cinye su.
Et elle a été brisée avec fureur; elle a été jetée à terre, et un vent brillant a flétri ses meilleures branches; ils se sont vengés d'elle, et la verge de sa puissance a été desséchée. Le feu l'a dévorée.
13 Yanzu an shuka ta a hamada, a busasshiyar ƙasa marar ruwa.
Et maintenant on l'a plantée dans le désert en une terre aride.
14 Wuta ta fito daga jikin rassanta ta cinye’ya’yanta. Babu sauran reshe mai ƙarfin da ya rage a kanta da ya dace da sandar mai mulki.’ Wannan waƙa ce kuma za a yi amfani da ita a matsayin makoki.”
Et une flamme est sortie d'une verge de ses meilleurs rameaux, et elle l'a dévorée, et elle n'eut plus la verge de sa puissance. Sa race est devenue une parabole de lamentation, une lamentation que l'on chantera.

< Ezekiyel 19 >