< Ezekiyel 18 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
І було́ мені слово Господнє таке:
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
„Що́ це вам, що ви складаєте припові́стку на Ізраїлеву землю, говорячи: „Батьки їли неспіле, а оско́ма в синів на зуба́х!“
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
Як живий Я, — говорить Господь Бог, — не бу́дете вже складати тієї припові́стки в Ізраїлі!
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
Тож усі душі Мої: як душа ба́тькова, так і душа синова — Мої вони! Душа, що грішить, — вона помре.
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
А чоловік, коли він справедливий, і робить право та справедливість,
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
на гора́х жертве́нного не їсть, і очей своїх не зводить до божкі́в Ізраїлевого дому, і жі́нки свого ближнього не занечищує, а до жінки в ча́сі її нечистоти́ не набли́жується,
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
і ніко́го не тисне, боржникові заста́ву його конче зверта́є, грабу́нку не чинить, хліб свій дає голодному, а голого покриває одежею,
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
на ли́хву не дає, а відсотків не бере, від кривди відверта́є руку свою, чинить правдивий суд поміж чоловіком та чоловіком,
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
уста́вами Моїми ходить, а прав Моїх дотримує, щоб чинити правду, — справедливий такий конче буде жити, говорить Господь Бог!
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
А як поро́дить він сина наси́льника, що кров проливає, і робить хоч тільки одне з того,
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
чого він усього того не робив, а також на гора́х жертве́нне їв, і жінку свого ближнього занечи́щував,
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
убогого й бідаря́ утискав, грабу́нки чинив, застави боржнико́ві не зверта́в, і до божкі́в зво́див свої очі, гидо́ту робив,
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
на ли́хву давав, і відсо́ток брав, — то чи буде він жити? Не буде він жити! Він усі ті гидо́ти чинив, — він мусить конче померти, кров його буде на ньо́му!
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
А ось породив він сина, і той побачив усі гріхи свого батька, які той робив, і хоч бачив, та не робив, як той:
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
на гора́х жертве́нного не їв, і очей своїх до божкі́в Ізраїлевого дому не зво́див, жінки свого ближнього не занечи́щував,
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
і ніко́го не утискав, заста́ви у за́став не брав, і грабунку не чинив, хліб свій голодному давав, а голого одежею покривав,
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
від кривди свою руку відверта́в, ли́хви та відсо́тків не брав, права́ Мої чинив, уста́вами Моїми ходив, — такий не помре за провину свого батька, — він конче буде жити!
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
Батько ж його, за те, що у́тиском тиснув, грабу́нком грабував брата, і що недобре чинив серед наро́ду свого, то ось він помре за провину свою!
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
А скажете ви: „Чому́ той син не поніс провину за батька?“Але ж син той чинив право та справедливість, дотримував усі устави Мої й виконував їх, — він конче буде жити!
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
Та душа, що грішить, вона помре. Син не понесе кари за ба́тькову провину, а ба́тько не понесе за провину си́нову, — справедливість справедливого буде на ньому, а несправедливість несправедливого на тому буде.
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
А коли б несправедливий відвернувся від усіх гріхів своїх, яких нароби́в, і вико́нував усі устави Мої, і робив право та справедли́вість, — буде конче він жити, не помре!
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
Усі його гріхи́, які наробив він, не згадаються йому, — він буде жити в своїй справедливості, яку чинив!
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
Чи Я маю вподо́бання в смерті несправедливого? — говорить Господь Бог, — чи ж не в тому, щоб він повернувся з доріг своїх та й жив?
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
А коли б справедливий відвернувся від своєї справедливости й став робити кривду, — усі ті гидо́ти, які робить несправедливий, то чи такий буде жити? Усі справедливості його, які він робив, не згадаються, — за своє спроневі́рення, що він спроневі́рив, і за гріх свій, що згрішив, за них він помре!
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
А ви кажете: „Непра́ва Господня дорога!“Послухайте но, доме Ізраїлів, чи ж дорога Моя неправа? Чи не ваші дороги неправі?
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
Коли б справедливий відверну́вся від своєї справедливости й чинив кривду, і за те помер, то він помре за кривду свою, яку він чинив.
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
А коли б несправедливий відвернувся від своєї несправедливости, яку він чинив, і чинив би право та справедливість, він душу свою при житті збереже́.
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
І коли б він побачив, і відвернувся від усіх своїх гріхів, які він чинив, то конче буде він жити, не помре!
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
А Ізраїлів дім каже: „Непра́ва Господня дорога!“Чи ж Мої дороги неправі, доме Ізраїлів? Чи ж то не ваші дороги неправі?
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
Тому́ буду судити вас, доме Ізраїлів, кожного за дорогами його, говорить Господь Бог. Покайтеся, і відверні́ться від усіх ваших гріхів, і не буде вам провина на спотика́ння!
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
Поскида́йте з себе всі ваші гріхи, якими ви грішили, і створіть собі нове́ серце та ново́го духа! І на́що маєте померти, Ізраїлів доме?
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
Бо не жадаю Я смерти помира́ючого, говорить Господь Бог, але покайтеся та й живіть!

< Ezekiyel 18 >