< Ezekiyel 18 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ponovno je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
»Kaj mislite, da uporabljate ta pregovor glede Izraelove dežele, rekoč: ›Očetje so jedli kislo grozdje, zobje otrok pa so skominasti?‹
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
Kakor jaz živim, ‹ govori Gospod Bog, ›nič več ne boste imeli priložnosti, da v Izraelu uporabljate ta pregovor.
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
Glejte, vse duše so moje; kakor očetova duša, tako je tudi sinova duša moja. Duša, ki greši, ta bo umrla.
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
Toda če je človek pravičen in dela to, kar je zakonito in pravilno
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
in ni jedel po gorah, niti ni svojih oči povzdigoval k malikom Izraelove hiše, niti ni omadeževal žene svojega soseda, niti ni prišel blizu ženski, ki ima menstruacijo,
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
in ni nikogar zatiral, temveč je dolžniku povrnil njegovo jamstvo, ni nikogar oplenil z nasiljem, svoj kruh dajal lačnemu in nagega pokrival z obleko;
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
ta, ki ni dajal za obresti, niti ni jemal nobenega dobička, ki je svojo roko umikal pred krivičnostjo, izvrševal pošteno sodbo med možem in možem,
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
hodil po mojih zakonih in se držal mojih sodb, da pravilno postopa; ta je pravičen, zagotovo bo živel, ‹ govori Gospod Bog.
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
›Če zaplodi sina ta, ki je ropar, prelivalec krvi in ki dela podobno katerikoli izmed teh stvari
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
in ki ne dela katerokoli izmed teh dolžnosti, temveč je celo jedel po gorah in omadeževal ženo svojega soseda,
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
zatiral revnega in pomoči potrebnega, plenil z nasiljem, ni povračal jamstva in svoje oči povzdigoval k malikom, zagrešil ogabnost,
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
dajal za obresti in jemal donos. Ali bo potem živel? Ta ne bo živel. Počenjal je vse te ogabnosti; zagotovo bo umrl; njegova kri bo na njem.
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
Torej glej, če zaplodi sina, ki vidi vse grehe svojega očeta, ki jih je storil in preudarja in ne dela temu podobno,
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
da ni jedel po gorah niti svojih oči ni povzdigoval k malikom Izraelove hiše, ni omadeževal žene svojega soseda
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
niti nobenega ni zatiral, ni zadrževal jamstva niti ni plenil z nasiljem, temveč je svoj kruh dajal lačnemu in nagega pokrival z obleko,
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
ki je zadrževal svoje roke pred [zatiranjem] revnega, ki ni prejemal obresti niti donosa, [ki je] izvrševal moje sodbe, hodil po mojih zakonih; ta ne bo umrl zaradi krivičnosti svojega očeta; zagotovo bo živel.
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
Kar se tiče njegovega očeta, ker je kruto zatiral, svojega brata plenil z nasiljem in med svojim ljudstvom počel to kar ni dobro, glej, celo ta bo umrl v svoji krivičnosti.
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
Vendar vi pravite: ›Zakaj? Ali sin ne nosi očetove krivičnosti? Kadar je sin storil, kar je zakonito in pravilno in se je držal vseh mojih zakonov in jih izvršil, bo zagotovo živel.
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
Duša, ki greši, ta bo umrla. Sin ne bo nosil očetove krivičnosti niti ne bo oče nosil sinove krivičnosti. Pravičnost pravičnega bo na njem in zlobnost zlobnega bo na njem.
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Toda če se bo zlobni obrnil od vseh svojih grehov, ki jih je zagrešil in se držal vseh mojih zakonov in storil to, kar je zakonito in pravilno, bo zagotovo živel, ne bo umrl.
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
Vsi njegovi prestopki, ki jih je zagrešil, mu ne bodo omenjeni. V svoji pravičnosti, ki jo je storil, bo živel.
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
Ali imam sploh kakšno zadovoljstvo, da bi zlobni umrl?‹ govori Gospod Bog: › in ne, da bi se vrnil iz svojih poti in živel?
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
Toda ko se pravični obrne proč od svoje pravičnosti in zagreši krivičnost in počne glede na vse ogabnosti, ki jih počne zloben človek, ali bo živel? Vsa njegova pravičnost, ki jo je storil, ne bo omenjena. V svojem prekršku, ki ga je prekršil in v svojem grehu, ki ga je zagrešil, v njima bo umrl.
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
Vendar vi pravite: ›Gospodova pot ni primerna.‹ Poslušaj sedaj, oh Izraelova hiša; mar moja pot ni primerna? Ali niso vaše poti neprimerne?
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
Ko se pravičen človek obrne proč od svoje pravičnosti in zagreši krivičnost in umira v njiju; zaradi svoje krivičnosti, ki jo je storil, bo umrl.
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
Ponovno, kadar se zloben človek obrne proč od svoje zlobnosti, ki jo je zagrešil in dela to, kar je zakonito in pravilno, bo svojo dušo rešil živo.
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Ker preudarja in se odvrača proč od vseh svojih prestopkov, ki jih je zagrešil, bo zagotovo živel, ne bo umrl.
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
Vendar Izraelova hiša pravi: ›Gospodova pot ni primerna.‹ Oh Izraelova hiša, mar moje poti niso primerne? Ali niso vaše poti neprimerne?
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
Zatorej vas bom sodil, oh Izraelova hiša, vsakogar glede na njegove poti, ‹ govori Gospod Bog. Pokesajte se in se obrnite od vseh svojih prestopkov; tako krivičnost ne bo vaš propad.
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
Od sebe odvrzite vse svoje prestopke, s katerimi ste se pregrešili in si naredite novo srce in novega duha, kajti zakaj hočete umreti, oh hiša Izraelova?
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
Kajti jaz nimam nobenega zadovoljstva v smrti tistega, ki umira, ‹ govori Gospod Bog: ›zatorej se obrnite in živite.‹

< Ezekiyel 18 >