< Ezekiyel 18 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A palavra de Yahweh veio até mim novamente, dizendo:
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
“O que você quer dizer, que você usa este provérbio a respeito da terra de Israel, dizendo “Os pais comeram uvas azedas, e os dentes das crianças estão no limite”?
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
“Como eu vivo”, diz o Senhor Javé, “você não usará mais este provérbio em Israel”.
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
Eis que todas as almas são minhas; como a alma do pai, assim também a alma do filho é minha”. A alma que pecar, ele morrerá.
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
“Mas se um homem é justo, e faz o que é lícito e correto,
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
e não comeu nas montanhas, não levantou os olhos para os ídolos da casa de Israel, não contaminou a esposa de seu vizinho, não se aproximou de uma mulher em sua impureza,
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
e não cometeu nenhum erro, mas restituiu ao devedor seu penhor, não levou nada por roubo, deu seu pão para os famintos, e cobriu a nua com uma peça de vestuário;
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
aquele que não emprestou a eles com interesse, não tirou nenhum aumento deles, que retirou sua mão da iniqüidade, tem feito verdadeira justiça entre o homem e o homem,
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
entrou em meus estatutos, e manteve minhas ordenações, para lidar verdadeiramente; ele é justo, ele certamente viverá”, diz o Senhor Yahweh.
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
“Se ele pai um filho que é um ladrão que derrama sangue, e que faz qualquer uma dessas coisas,
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
ou que não faz nenhuma dessas coisas mas tem comido nos santuários da montanha e contaminou a esposa de seu vizinho, O site
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
prejudicou os pobres e necessitados, foi levado por roubo, não restaurou a promessa, e levantou seus olhos para os ídolos, cometeu abominação,
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
tem emprestado com interesse, e tem tirado aumento dos pobres, viverá ele então? Ele não viverá. Ele já fez todas essas abominações. Ele certamente morrerá. Seu sangue estará sobre ele.
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
“Agora, eis que, se ele pai um filho que vê todos os pecados de seu pai que ele fez, e teme, e não faz o mesmo,
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
que ainda não comeu nas montanhas, não levantou os olhos para os ídolos da casa de Israel, não contaminou a esposa de seu vizinho,
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
não cometeu nenhum erro, não levou nada para se comprometer, não foi levado por roubo, mas deu seu pão para os famintos, e cobriu a nua com uma peça de vestuário;
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
que retirou sua mão dos pobres, que não tenha recebido juros ou aumento, executou minhas ordenações, entrou em meus estatutos; ele não morrerá pela iniqüidade de seu pai. Ele certamente viverá.
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
Quanto a seu pai, porque ele oprimiu cruelmente, roubou seu irmão e fez o que não é bom entre seu povo, eis que ele morrerá em sua iniqüidade.
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
“No entanto você diz: “Por que o filho não suporta a iniqüidade do pai? Quando o filho tiver feito o que é legal e correto, e tiver cumprido todos os meus estatutos, e os tiver feito, ele certamente viverá.
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
A alma que pecar, ele morrerá. O filho não levará a iniqüidade do pai, nem o pai levará a iniqüidade do filho. A justiça dos justos recairá sobre ele, e a maldade dos ímpios recairá sobre ele.
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
“Mas se o ímpio se converter de todos os seus pecados que cometeu, e guardar todos os meus estatutos, e fizer o que é lícito e correto, certamente viverá. Ele não morrerá.
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
Nenhuma de suas transgressões que ele cometeu será lembrada contra ele. Em sua justiça que ele fez, ele viverá.
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
Tenho algum prazer na morte do ímpio?” diz o Senhor Javé, “e não antes que ele volte de seu caminho, e viva?
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
“Mas quando o justo se afasta de sua justiça e comete iniqüidade, e faz de acordo com todas as abominações que o ímpio faz, deveria ele viver? Nenhuma de suas ações justas que ele tenha feito será lembrada. Em sua transgressão que cometeu, e em seu pecado que cometeu, morrerá neles.
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
“No entanto, você diz: 'O caminho do Senhor não é igual'. Ouça agora, casa de Israel: O meu caminho não é igual? Seus caminhos não são desiguais?
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
Quando o homem justo se afasta de sua justiça, e comete iniqüidade, e morre nela, então ele morre em sua iniqüidade que ele fez.
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
Novamente, quando o homem mau se afasta de sua maldade que cometeu, e faz o que é lícito e correto, ele salvará sua alma viva.
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Porque ele considera, e se afasta de todas as suas transgressões que cometeu, certamente viverá. Ele não morrerá.
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
No entanto, a casa de Israel diz: “O caminho do Senhor não é justo”. Casa de Israel, não são justos os meus caminhos? Seus caminhos não são injustos?
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
“Portanto, eu vos julgarei, casa de Israel, todos de acordo com seus caminhos”, diz o Senhor Yahweh. “Voltai, e convertei-vos de todas as vossas transgressões, assim a iniqüidade não será a vossa ruína”.
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
Lançai de vós todas as vossas transgressões em que transgredistes; e fazei de vós um coração novo e um espírito novo”. Por que morrereis, casa de Israel?
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
Pois não tenho prazer na morte daquele que morre”, diz o Senhor Yahweh. “Portanto, convertei-vos, e vivei!

< Ezekiyel 18 >