< Ezekiyel 18 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۱
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
«شما چه‌کار دارید که این مثل رادرباره زمین اسرائیل می‌زنید و می‌گویید: پدران انگور ترش خوردند و دندانهای پسران کندگردید.»۲
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
خداوند یهوه می‌گوید: «به حیات خودم قسم که بعد از این این مثل را در اسرائیل نخواهیدآورد.۳
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
اینک همه جانها از آن منند چنانکه جان پدر است، همچنین جان پسر نیز، هردوی آنها ازآن من می‌باشند. هر کسی‌که گناه ورزد او خواهدمرد.۴
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
و اگر کسی عادل باشد و انصاف و عدالت رابعمل آورد،۵
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
و بر کوهها نخورد و چشمان خودرا بسوی بتهای خاندان اسرائیل برنیفرازد و زن همسایه خود را بی‌عصمت نکند و به زن حایض نزدیکی ننماید،۶
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
و بر کسی ظلم نکند و گروقرضدار را به او رد نماید و مال کسی را به غصب نبرد، بلکه نان خود را به گرسنگان بدهد وبرهنگان را به‌جامه بپوشاند،۷
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
و نقد را به سودندهد و ربح نگیرد، بلکه دست خود را از ستم برداشته، انصاف حقیقی را در میان مردمان اجرادارد،۸
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و به فرایض من سلوک نموده و احکام مرانگاه داشته، به راستی عمل نماید. خداوند یهوه می‌فرماید که آن شخص عادل است و البته زنده خواهد ماند.۹
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
«اما اگر او پسری ستم پیشه و خونریز تولیدنماید که یکی از این کارها را بعمل آورد،۱۰
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
وهیچکدام از آن اعمال نیکو را بعمل نیاورد بلکه برکوهها نیز بخورد و زن همسایه خود را بی‌عصمت سازد،۱۱
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
و بر فقیران و مسکینان ظلم نموده، مال مردم را به غصب ببرد و گرو را پس ندهد، بلکه چشمان خود را بسوی بتها برافراشته، مرتکب رجاسات بشود،۱۲
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
و نقد را به سود داده، ربح گیرد، آیا او زنده خواهد ماند؟ البته او زنده نخواهد ماند و به‌سبب همه رجاساتی که بجاآورده است خواهد مرد و خونش بر سرش خواهد بود.۱۳
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
«و اگر پسری تولید نماید که تمامی گناهان را که پدرش بجا می‌آورد دیده، بترسد و مثل آنهاعمل ننماید،۱۴
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
و بر کوهها نخورد و چشمان خود را بسوی بتهای خاندان اسرائیل برنیفرازد وزن همسایه خویش را بی‌عصمت نکند،۱۵
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
و برکسی ظلم نکند و گرو نگیرد و مال احدی را به غصب نبرد بلکه نان خود را به گرسنگان دهد وبرهنگان را به‌جامه پوشاند،۱۶
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
و دست خود را ازفقیران برداشته، سود و ربح نگیرد و احکام مرا بجاآورده، به فرایض من سلوک نماید، او به‌سبب گناه پدرش نخواهد مرد بلکه البته زنده خواهد ماند.۱۷
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
و اما پدرش چونکه با برادران خود به شدت ظلم نموده، مال ایشان را غصب نمود و اعمال شنیع را در میان قوم خود بعمل آورد او البته به‌سبب گناهانش خواهد مرد.۱۸
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
«لیکن شما می‌گویید چرا چنین است؟ آیاپسر متحمل گناه پدرش نمی باشد؟ اگر پسرانصاف و عدالت را بجا آورده، تمامی فرایض مرانگاه دارد و به آنها عمل نماید، او البته زنده خواهد ماند.۱۹
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
هر‌که گناه کند او خواهد مرد. پسر متحمل گناه پدرش نخواهد بود و پدرمتحمل گناه پسرش نخواهد بود. عدالت مردعادل بر خودش خواهد بود و شرارت مرد شریربر خودش خواهد بود.۲۰
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
«و اگر مرد شریر از همه گناهانی که ورزیده باشد بازگشت نماید و جمیع فرایض مرا نگاه داشته، انصاف و عدالت را بجا آورد او البته زنده مانده نخواهد مرد.۲۱
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
تمامی تقصیرهایی که کرده باشد به ضد او به یاد آورده نخواهد شد بلکه در عدالتی که کرده باشد زنده خواهد ماند.»۲۲
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
خداوند یهوه می‌فرماید: «آیا من از مردن مرد شریر مسرور می‌باشم؟ نی بلکه از اینکه ازرفتار خود بازگشت نموده، زنده ماند.۲۳
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
و اگرمرد عادل از عدالتش برگردد و ظلم نموده، موافق همه رجاساتی که شریران می‌کنند عمل نماید آیااو زنده خواهد ماند؟ نی بلکه تمامی عدالت او که کرده است به یاد آورده نخواهد شد و در خیانتی که نموده و در گناهی که ورزیده است خواهدمرد.۲۴
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
«اما شما می‌گویید که طریق خداوندموزون نیست. پس حال‌ای خاندان اسرائیل بشنوید: آیا طریق من غیر موزون است و آیاطریق شما غیر موزون نیست؟۲۵
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
چونکه مردعادل از عدالتش برگردد و ظلم کند در آن خواهدمرد. به‌سبب ظلمی که کرده است خواهد مرد.۲۶
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
و چون مرد شریر را از شرارتی که کرده است بازگشت نماید و انصاف و عدالت را بجا آورد، جان خود را زنده نگاه خواهد داشت.۲۷
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
چونکه تعقل نموده، از تمامی تقصیرهایی که کرده بودبازگشت کرد البته زنده خواهد ماند و نخواهدمرد.۲۸
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
لیکن شما‌ای خاندان اسرائیل می‌گوییدکه طریق خداوند موزون نیست. ای خاندان اسرائیل آیا طریق من غیر موزون است و آیاطریق شما غیر موزون نیست؟»۲۹
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
بنابراین خداوند یهوه می‌گوید: «ای خاندان اسرائیل من برهریک از شما موافق رفتارش داوری خواهم نمود. پس توبه کنید و از همه تقصیرهای خودبازگشت نمایید تا گناه موجب هلاکت شما نشود.۳۰
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
تمامی تقصیرهای خویش را که مرتکب آنها شده‌اید از خود دور اندازید و دل تازه و روح تازه‌ای برای خود ایجاد کنید. زیرا که‌ای خاندان اسرائیل برای چه بمیرید؟۳۱
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
زیرا خداوند یهوه می‌گوید: من از مرگ آنکس که می‌میرد مسرورنمی باشم. پس بازگشت نموده، زنده مانید.»۳۲

< Ezekiyel 18 >