< Ezekiyel 18 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de Yahvé me fut adressée de nouveau, en disant:
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
« Que veux-tu dire par là, que tu utilises ce proverbe concernant le pays d'Israël, en disant, Les pères ont mangé des raisins aigres, et les enfants ont les dents serrées »?
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
« Je suis vivant », dit le Seigneur Yahvé, « vous n'utiliserez plus ce proverbe en Israël.
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
Voici, toutes les âmes sont à moi; comme l'âme du père, ainsi l'âme du fils est à moi. L'âme qui pèche, c'est elle qui mourra.
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
« Mais si un homme est juste, et fait ce qui est légal et juste,
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
et n'a pas mangé sur les montagnes, n'a pas levé les yeux vers les idoles de la maison d'Israël, n'a pas souillé la femme de son voisin, ne s'est pas approché d'une femme dans son impureté,
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
et n'a fait de tort à personne, mais a rendu au débiteur son gage, n'a rien pris par vol, a donné son pain aux affamés, et a couvert le nu d'un vêtement;
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
celui qui ne leur a pas prêté avec intérêt, n'a pas pris d'augmentation de leur part, qui a retiré sa main de l'iniquité, a exécuté la vraie justice entre l'homme et l'homme,
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
a marché dans mes statuts, et a gardé mes ordonnances, pour traiter véritablement; il est juste, il vivra », dit le Seigneur Yahvé.
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
« S'il engendre un fils qui est un voleur et qui verse le sang, et qui fait l'une de ces choses,
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
ou qui ne fait aucune de ces choses. mais a mangé dans les sanctuaires de la montagne et a souillé la femme de son voisin,
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
a fait du tort aux pauvres et aux nécessiteux, a pris par vol, n'a pas rétabli l'engagement, et a levé les yeux vers les idoles, a commis une abomination,
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
a prêté avec intérêt, et a pris l'argent des pauvres, vivra-t-il alors? Il ne vivra pas. Il a commis toutes ces abominations. Il mourra sûrement. Son sang sera sur lui.
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
« Or, voici, s'il engendre un fils qui voit tous les péchés de son père, qu'il a commis, et qui a peur, il ne fait pas de même,
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
qui n'a pas mangé sur les montagnes, n'a pas levé les yeux vers les idoles de la maison d'Israël, n'a pas souillé la femme de son voisin,
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
Le na fait de tort à personne, n'a pas pris de gage, n'a pas été prise en flagrant délit de vol, mais a donné son pain aux affamés, et a couvert le nu d'un vêtement;
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
qui a retiré sa main des pauvres, qui n'a pas reçu d'intérêt ou d'augmentation, a exécuté mes ordonnances, a marché dans mes statuts; il ne mourra pas pour l'iniquité de son père. Il vivra certainement.
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
Quant à son père, parce qu'il a opprimé cruellement, dépouillé son frère, et fait ce qui n'est pas bien au milieu de son peuple, voici, il mourra dans son iniquité.
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
Et vous dites: « Pourquoi le fils ne porte-t-il pas l'iniquité du père? Quand le fils aura fait ce qui est licite et juste, quand il aura observé toutes mes lois et les aura mises en pratique, il vivra.
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
L'âme qui pèche, elle, mourra. Le fils ne portera pas l'iniquité du père, et le père ne portera pas l'iniquité du fils. La justice des justes sera sur lui, et la méchanceté des méchants sera sur lui.
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
« Mais si le méchant se détourne de tous les péchés qu'il a commis, s'il observe toutes mes lois, s'il fait ce qui est licite et juste, il vivra. Il ne mourra pas.
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
On ne se souviendra pas contre lui des fautes qu'il a commises. Il vivra selon la justice qu'il a pratiquée.
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
Est-ce que je prends plaisir à la mort du méchant, dit le Seigneur Yahvé, et ne préfère-t-il pas qu'il revienne de sa voie et qu'il vive?
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
« Mais quand le juste se détourne de sa justice, qu'il commet l'iniquité et qu'il se conforme à toutes les abominations que fait le méchant, doit-il vivre? On ne se souviendra d'aucune des actions justes qu'il a accomplies. Il mourra de la faute qu'il a commise et du péché qu'il a commis.
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
« Et vous dites: 'La voie du Seigneur n'est pas égale'. Écoutez maintenant, maison d'Israël: Ma voie n'est-elle pas égale? Vos voies ne sont-elles pas inégales?
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
Si le juste se détourne de sa justice, commet l'iniquité et meurt par elle, il meurt par l'iniquité qu'il a commise.
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
De même, si le méchant se détourne de la méchanceté qu'il a commise et fait ce qui est licite et juste, il sauvera son âme en vie.
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Parce qu'il réfléchit et se détourne de toutes les transgressions qu'il a commises, il vivra. Il ne mourra pas.
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
Mais la maison d'Israël dit: « La voie de l'Éternel n'est pas droite ». Maison d'Israël, mes voies ne sont-elles pas équitables? Tes voies ne sont-elles pas injustes?
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
« C'est pourquoi je vous jugerai, maison d'Israël, chacun selon ses voies, dit le Seigneur Yahvé. « Revenez, et détournez-vous de toutes vos transgressions, afin que l'iniquité ne soit pas votre ruine.
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
Rejetez loin de vous toutes les transgressions que vous avez commises, et faites-vous un cœur nouveau et un esprit nouveau. Car pourquoi mourrez-vous, maison d'Israël?
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
Car je ne prends aucun plaisir à la mort de celui qui meurt, dit le Seigneur Yahvé. « C'est pourquoi tournez-vous, et vivez!