< Ezekiyel 18 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Jehovah came to me again, saying:
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
What mean ye, that ye use this proverb concerning the land of Israel, saying, “The fathers have eaten sour grapes, and the children's teeth are set on edge”?
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
As I live, saith the Lord Jehovah, ye shall not have occasion any more to use this proverb in Israel.
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
Behold, all souls are mine; as the soul of the father, so also the soul of the son, is mine; the soul that sinneth, it shall die.
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
But if a man be just, and do that which is lawful and right;
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
if he eat not upon the mountains, and lift not up his eyes to the idols of the house of Israel, and defile not his neighbor's wife, and come not near a woman during her uncleanness;
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
if he oppress not any, if he restore to the debtor his pledge, spoil none by violence, give his bread to the hungry, and cover the naked with a garment;
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
if he give not forth upon usury, and take not increase; if he withdraw his hand from iniquity, and give true judgment between man and man;
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
if he walk in my statutes and keep my commandments, to deal uprightly, —he is just; he shall surely live, saith the Lord Jehovah.
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
But if he have a son that is a robber, a shedder of blood, and that doeth to his brother any of these things,
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
and doeth not all those duties, but eateth upon the mountains, and defileth his neighbor's wife,
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
oppresseth the poor and needy, spoileth by violence, restoreth not the pledge, lifteth up his eyes to idols, and committeth abomination,
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
giveth forth upon usury, and taketh increase, shall he live? No! he shall not live. He hath done all these abominations; he shall surely die; his blood shall be upon him.
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
Yet lo, if he have a son that seeth all the sins which his father committed, that seeth them and doeth not such like,
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
that eateth not upon the mountains, nor lifteth up his eyes to the idols of the house of Israel, nor defileth his neighbor's wife,
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
nor oppresseth any, nor taketh a pledge, nor spoileth by violence, but giveth his food to the hungry, and covereth the naked with a garment,
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
keepeth back his hand from the poor, and taketh no usury or increase, keepeth my commandments, and walketh in my statutes, he shall not die for the iniquity of his father; he shall surely live.
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
As for his father, because he cruelly oppressed, spoiled his brother by violence, and did that which is not good among his people, lo, he shall die for his iniquity.
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
Yet say ye, “Why? Doth not the son bear the iniquity of the father?” When the son doeth that which is lawful and right, keepeth all my statutes and doeth them, he shall surely live.
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
The soul that sinneth, it shall die. The son shall not bear the iniquity of the father, neither shall the father bear the iniquity of the son. The righteousness of the righteous shall be upon him, and the wickedness of the wicked shall be upon him.
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
But if the wicked will turn from all his sins which he hath committed, and keep all my statutes, and do that which is lawful and right, he shall surely live, he shall not die.
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
None of his transgressions which he hath committed shall be remembered unto him; for his righteousness, which he hath done, he shall live.
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
Have I any pleasure at all that the wicked should die, saith the Lord Jehovah, and not that he should turn from his ways and live?
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
But when the righteous turneth from his righteousness, and committeth iniquity, and doeth according to all the abominations which the wicked man doeth, shall he live? All his righteousness which he hath done shall not be remembered; for his trespass which he hath trespassed, and for his sin which he hath sinned, for them shall he die.
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
Yet ye say, “The way of the Lord is not right.” Hear now, O house of Israel! “Is not my way right?” Is it not your ways that are not right?
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
When a righteous man turneth from his righteousness, and committeth iniquity, and on this account dieth, for his iniquity which he hath done doth he die.
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
And when the wicked man turneth from his iniquity which he hath committed, and doeth that which is lawful and right, he shall save his soul alive.
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Because he considereth and turneth from all his transgressions which he hath committed, he shall surely live, he shall not die.
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
Yet saith the house of Israel, “The way of the Lord is not right.” O house of Israel, are not my ways right? Is it not your ways that are not right?
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
Therefore I will judge you, O house of Israel, every one according to his ways, saith the Lord Jehovah. Turn ye, turn yourselves from all your transgressions, so that iniquity may not be your ruin.
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
Cast away from you all your transgressions which ye have committed, and make you a new heart, and a new spirit! For why will ye die, O house of Israel?
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
For I have no pleasure in the death of him that dieth, saith the Lord Jehovah. Wherefore turn yourselves and live!