< Ezekiyel 18 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Opět stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
2 “Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
Což jest vám, že užíváte přísloví tohoto o zemi Izraelské, říkajíce: Otcové jedli hrozen trpký, a zubové synů laskominy mají?
3 “Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
Živť jsem já, praví Panovník Hospodin, že nebudete moci více užívati přísloví tohoto v Izraeli.
4 Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
Aj, všecky duše mé jsou, jakož duše otcova, tak i duše synova mé jsou. Duše, kteráž hřeší, ta umře.
5 “A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
Nebo byl-li by někdo spravedlivý, a činil by soud a spravedlnost;
6 ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
Na horách by nejídal, a očí svých nepozdvihoval k ukydaným bohům domu Izraelského, a manželky bližního svého by nepoškvrnil, a k ženě pro nečistotu oddělené nepřistoupil;
7 Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
Kterýž by žádného neutiskal, základ dlužníku svému by navracoval, cizího mocí nebral, chleba svého by lačnému udílel, a nahého přiodíval rouchem;
8 Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
Na lichvu by nedával, a úroku nebral, od nepravosti ruku svou by odvracoval, soud pravý mezi jedním i druhým by činil;
9 Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
V ustanoveních mých by chodil, a soudů mých ostříhal, čině, což pravého jest: spravedlivý ten jistě žeť živ bude, praví Panovník Hospodin.
10 “A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
Zplodil-li by pak syna lotra, prolevače krve, kterýž by čímkoli z těch věcí škodil bratru,
11 (ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
Onoho pak všeho nečinil by, anobrž i na horách by jídal, a ženy bližního svého by poškvrnil;
12 Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
Chudého a nuzného by utiskl, cizí věci mocí vzal, základu by nenavrátil, a k ukydaným bohům očí svých by pozdvihoval, ohavnost provodil,
13 Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
Na lichvu by dával, a úrok bral: zdaž bude živ? Nebude živ. Poněvadž všecky ohavnosti tyto činil, jistotně umře, krev jeho přijde na něj.
14 “Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
A aj, zplodil-li by syna, kterýž by spatřil všecky hříchy otce svého, kteréž činil, a vida, nečinil by tak;
15 “Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
Na horách by nejídal, a očí svých nepozdvihoval k ukydaným bohům domu Izraelského, manželky bližního svého by nepoškvrnil,
16 Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
A aniž by koho utiskal, základu by nezadržoval, cizího mocí nebral, chleba svého lačnému by udílel, a nahého rouchem by přiodíl;
17 Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
Od chudého by zdržel ruku svou, lichvy a úroku by nebral, soudy mé činil, v ustanoveních mých by chodil: tenť neumře pro nepravost otce svého, jistě živ bude.
18 Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
Otec pak jeho, proto že se bezpráví dopouštěl, cizí věci bratru mocí bral, a to, což není dobré, činil u prostřed lidu svého: protož aj, umře pro nepravost svou.
19 “Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
Ale říkáte: Jak by to bylo? Zdaž nenese syn nepravosti otcovy? Když syn činí soud a spravedlnost, všech ustanovení mých ostříhá a činí je, jistě žeť živ bude.
20 Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
Duše, kteráž hřeší, ta umře. Syn neponese nepravosti otcovy, aniž otec ponese nepravosti synovy; spravedlnost spravedlivého při něm zůstane, též bezbožnost bezbožného na něj připadne.
21 “Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Pakli byse bezbožný odvrátil ode všech hříchu svých, kteréž činil, a ostříhal by všech ustanovení mých, a činil by soud a spravedlnost, jistě živ bude a neumře.
22 Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
Žádná přestoupení jeho, jichž se dopustil, nebudou jemu připomínána; v spravedlnosti své, kterouž by činil, živ bude.
23 Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
Zdaliž jakou líbost mám, když umírá bezbožný? dí Panovník Hospodin. Zdali ne raději když se odvrací od cest svých, aby živ byl?
24 “Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
Pakli by se odvrátil spravedlivý od spravedlnosti své, a činil by nepravost, čině podlé všech ohavností, kteréž činí bezbožný, takový-liž by živ byl? Na žádné spravedlnosti jeho, kteréž činil, nebude pamatováno. Pro přestoupení své, jehož se dopouštěl, a pro hřích svůj, kterýž páchal, pro tyť věci umře.
25 “Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
Že pak říkáte: Není pravá cesta Páně, poslyštež nyní, ó dome Izraelský: Zdali má cesta není pravá? Zdali nejsou cesty vaše nepravé?
26 In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
Když by se odvrátil spravedlivý od spravedlnosti své, a čině nepravost, v tom by umřel, pro nepravost svou, kterouž činil, umře.
27 Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
A když by se odvrátil bezbožný od bezbožnosti své, kterouž činil, a činil by soud a spravedlnost, tenť duši svou zachová při životu.
28 Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
Nebo prohlédl, a odvrátil, se ode všech přestoupení svých, jichž se dopouštěl; jistě žeť živ bude a neumře.
29 Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
A však vždy říká dům Izraelský: Není pravá cesta Páně. Zdali mé cesty nepravé jsou, ó dome Izraelský? Zdaliž nejsou cesty vaše nepravé?
30 “Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
A protož každého z vás podlé cest jeho souditi budu, ó dome Izraelský, dí Panovník Hospodin. Navraťtež se a odvraťte ode všech přestoupení svých, aby vám nebyla k úrazu nepravost.
31 Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
Odvrzte od sebe všecka přestoupení vaše, jichž jste se dopouštěli, a učiňte sobě srdce nové a ducha nového. I pročež mřete, ó dome Izraelský?
32 Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!
Však nemám líbosti v smrti toho, jenž umírá, dí Panovník Hospodin. Obraťte se tedy, a živi buďte.