< Ezekiyel 17 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
И бысть слово Господне ко мне глаголя:
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
сыне человечь, повеждь повесть и рцы притчу на дом Израилев,
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
и речеши: сия глаголет Адонаи Господь: орел великий, великокрилый, долгий протяжением, исполнь ногтей, иже имать повеление внити в Ливан, и взя избранныя кедра,
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
и верхи мягкости острога, и принесе я в землю Хананейску, во граде огражденнем положи я:
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
и взя от семене земнаго и даде е на поли плодне, (да утвердит корение) над водами многими, видено учини е:
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
и прозябе и бысть в виноград немощен и мал величеством, еже являтися лозию его на нем, и корение его под ним бяше: и бысть в виноград, и сотвори розги, и простре отрасли своя.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
И бысть орел другий велик, великокрилный, мног ногтьми, и се, виноград сей оплетаяся об нем: и корение его к нему, и лозие свое испусти ему, еже напаяти себе со грудием сада своего.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
На поли добре, на воде мнозе питается той, еже сотворити прозябения и приносити плод, еже быти в виноград велик.
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Сего ради рцы: сия глаголет Адонаи Господь: еда исправится? Не корение ли мягкоты его и плод изгниет? И изсхнут вся леторасли его, и не мышцею ли великою, ни людьми многими еже исторгнути его из корения его?
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
И се, тыет: еда успеет? Не абие ли, егда коснется ему ветр знойный, посхнет сухотою? Со грудием прозябения своего изсхнет.
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
И бысть слово Господне ко мне глаголя:
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
сыне человечь, рцы ко дому прогневляющему мя: не весте ли, что суть сия? Рцы им: се, грядет царь Вавилонск на Иерусалим, и возмет царя его и князя его, и отведет я к себе в Вавилон:
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
и поймет от племене царска, и завещает с ним завет, и введет его в клятве, и старейшины земли возмет,
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
еже быти в царство немощно, еже весьма не возноситися, (но) хранити завет его и стояти в нем:
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
и отвержется от него посылая послы своя во Египет дати ему кони и люди многи: еда исправит? Спасется ли творяй сопротивная? И преступаяй завет спасется ли?
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
Живу Аз, глаголет Адонаи Господь, аще не на месте, идеже царь воцаривый его, иже похули клятву Мою и иже преступи завет Мой, с ним среде Вавилона скончается.
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
И не в силе велицей, ниже в народе мнозе сотворит с ним фараон брань во острозе и в сограждении стрельниц, еже изяти душы многи.
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
И похули клятву, еже преступити завет, и се, даде руку свою и вся сия сотвори ему: не спасется.
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
Сего ради рцы: сия глаголет Адонаи Господь: живу Аз, аще не клятву Мою, юже похули, и завет Мой, егоже преступи, дам на главу его:
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
и простру мрежу Мою нань, и ят будет во одержании ея: и приведу его в Вавилон и разсуждуся с ним тамо о неправде его, еюже неправдова ко Мне:
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
и вси избегшии его и вси избраннии со всеми ополчении его мечем падут, и вся оставшая их разсею по всему ветру, и увесте, яко Аз Господь глаголах.
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
Сего ради сия глаголет Адонаи Господь: и возму Аз от избранных кедра высокаго от верха и дам от главы отраслей его, сердца их остружу и насажду аз на горе высоце:
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
и повешу и в горе высоце Израилеве и насажду и, и прорастит отрасль и сотворит плод и будет в кедр велик: и почиет под ним всяк зверь, и под сению его почиет всяка птица, и лозие его паки устроятся:
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
и увесть всяко древо полевое, яко Аз Господь смиряяй древо высокое и возносяй древо смиренное, и изсушаяй древо зеленое и проращаяй древо сухое: Аз Господь глаголах и сотворю.

< Ezekiyel 17 >