< Ezekiyel 17 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut encore adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
Fils de l'homme, propose une énigme, présente une parabole à la maison d'Israël.
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
Tu diras: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Un grand aigle, aux grandes ailes, aux ailes étendues, tout couvert d'un duvet de couleurs variées, vint sur le Liban et enleva la cime d'un cèdre.
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
Il arracha le plus élevé de ses rameaux, le transporta en un pays marchand, et le déposa dans une ville de commerce.
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
Il prit ensuite du plant du pays et le confia à un sol fertile; il le plaça près des eaux abondantes et le planta comme un saule.
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
Le plant poussa, devint un cep de vigne étendu, mais peu élevé; ses rameaux étaient tournés du côté de l'aigle, et ses racines étaient sous lui; il devint un cep, produisit des sarments et donna du feuillage.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
Mais il y avait un autre grand aigle, aux grandes ailes, au plumage épais; et voici, des couches où il était planté, le cep étendit vers lui ses racines, et dirigea ses rameaux de son côté, afin qu'il l'arrosât.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
Et pourtant il était planté dans un bon terrain, près d'eaux abondantes, de manière à produire des sarments, à porter du fruit et à devenir un cep superbe.
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Dis: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Le cep réussira-t-il? Le premier aigle n'en arrachera-t-il pas les racines, et n'en coupera-t-il pas les fruits, de manière à faire sécher tous les rejetons qu'il aura produits? Il séchera, et il n'y aura besoin ni d'un grand effort, ni de beaucoup de gens pour le séparer de ses racines.
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
Voici, il est planté; mais réussira-t-il? Dès que le vent d'orient le touchera, ne séchera-t-il pas entièrement? Il séchera sur les couches où il a été planté.
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
Dis à cette maison rebelle: Ne savez-vous pas ce que signifient ces choses? Dis: Voici, le roi de Babylone est allé à Jérusalem; il a pris le roi et les principaux, et les a emmenés avec lui à Babylone.
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
Et il a pris un rejeton de la race royale, il a fait alliance avec lui et lui a fait prêter serment; et il s'est emparé des puissants du pays,
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
Afin que le royaume fût tenu dans l'abaissement, sans pouvoir s'élever, tout en le laissant subsister, s'il observait son alliance.
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
Mais il s'est révolté contre lui, en envoyant des ambassadeurs en Égypte, afin qu'on lui donnât des chevaux et un grand nombre d'hommes. Pourra-t-il réussir, échapper, celui qui a fait de telles choses? Il a rompu l'alliance, et il échapperait!
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
Je suis vivant! dit le Seigneur, l'Éternel, c'est dans la résidence du roi qui l'a fait régner, dont il a méprisé le serment et rompu l'alliance, c'est près de lui, au milieu de Babylone, qu'il mourra!
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
Et Pharaon, avec une grande armée et des troupes nombreuses, ne fera rien pour lui dans la guerre, quand on aura élevé des remparts et construit des tours pour faire périr nombre d'âmes.
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
Car il a méprisé le serment, en violant l'alliance; et voici, après avoir donné sa main, il a néanmoins fait toutes ces choses. Il n'échappera pas!
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
C'est pourquoi, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Je suis vivant! c'est mon serment qu'il a méprisé, mon alliance qu'il a rompue; je ferai retomber cela sur sa tête.
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
J'étendrai mon rets sur lui, et il sera pris dans mes filets; je l'emmènerai à Babylone où je plaiderai contre lui sur sa perfidie à mon égard.
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
Et tous les fuyards de toutes ses troupes tomberont par l'épée; et ceux qui resteront seront dispersés à tous les vents. Et vous saurez que c'est moi, l'Éternel, qui ai parlé.
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Je prendrai moi-même la cime d'un cèdre élevé, et je la planterai. De l'extrémité de ses rameaux, je couperai un tendre rejeton, et moi-même je le planterai sur une montagne haute et élevée.
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
Sur la haute montagne d'Israël, je le planterai; il poussera des jets, et produira des fruits; il deviendra un cèdre magnifique, et des oiseaux de toute espèce viendront s'abriter sous lui; tout ce qui a des ailes habitera à l'ombre de ses rameaux.
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
Et tous les arbres des champs connaîtront que, moi l'Éternel, j'ai abaissé l'arbre élevé, et élevé le petit arbre, que j'ai fait sécher l'arbre vert et fait reverdir l'arbre sec. Moi l'Éternel, je l'ai dit, et je le ferai.