< Ezekiyel 17 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Yahweh came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
“Son of man, present a riddle and speak a parable to the house of Israel.
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
Say, 'The Lord Yahweh says this: A large eagle with large wings and long pinions, full of feathers, and that was multicolored went to Lebanon and took hold of the top of a cedar tree.
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
It broke off the tips of the branches and took them to the land of Canaan; he planted it in a city of merchants.
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
He also took some seed of the land and planted it in fertile soil. He placed it beside a large body of water like a willow.
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
Then it sprouted and became a spreading vine low to the ground. Its branches turned toward him, and its roots grew under it. So it became a vine and produced branches and sent out shoots.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
But there was another great eagle with large wings and many feathers. Behold! This vine turned its roots toward the eagle, and it spread out its branches toward the eagle from the place it had been planted so it would be watered.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
It had been planted in good soil beside a large body of water so it would produce branches and sprout fruit, to become a magnificent vine.'
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Say to the people, 'The Lord Yahweh says this: Will it prosper? Will it not be uprooted and stripped of its fruit so that it withers, and all its fresh growth will wither? No strong arm or many people will be needed to pull it out by its roots.
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
So behold! After it has been planted, will it grow? Will it not wither when the eastern wind touches it? It will completely wither away in the garden plot where it sprouted.'”
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of Yahweh came to me, saying,
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
“Speak to the rebellious house, 'Do you not know what these things mean? Behold! The king of Babylon came to Jerusalem and took her king and her princes and brought them to him in Babylon.
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
Then he took a royal descendant, made a covenant with him, and brought him under an oath. He took away the powerful people of the land,
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
so the kingdom might become lowly and not lift itself up. By keeping his covenant the land will survive.
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
But the king of Jerusalem rebelled against him by sending his ambassadors to Egypt to acquire horses and an army. Will he succeed? Will the one doing these things escape? If he breaks the covenant, will he escape?
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
As I live!—this is the Lord Yahweh's declaration—he will surely die in the land of the king who made him king, the king whose oath he despised, and whose covenant he broke. He will die in the middle of Babylon.
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
Pharaoh with his mighty army and a great company of men will not help him in battle, when ramps are constructed and siege walls are built up to cut off many lives.
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
For the king despised his oath by breaking the covenant. Behold, he reached out with his hand to make a promise and yet he did all these things. He will not escape.
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
Therefore the Lord Yahweh says this: As I live, was it not my oath that he despised and my covenant that he broke? So I will bring his punishment on his head!
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
I will spread my net out over him, and he will be caught in my hunting net. Then I will bring him to Babylon and execute judgment on him there for his treason that he committed when he betrayed me!
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
All of his refugees in his armies will fall by the sword, and the ones who remain will be scattered in every direction. Then you will know that I am Yahweh; I have declared this would happen.”
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
The Lord Yahweh says this, 'So I myself will take away the highest part of the cedar tree, and I will plant it away from its tender branches. I will break it off, and I myself will plant it on a high mountain.
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
I will plant it on the mountains of Israel so it will bear branches and produce fruit, and it will become a majestic cedar so that every winged bird will live under it. They will nest in the shade of its branches.
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
Then all the trees of the field will know that I am Yahweh. I bring down the high trees and I raise up the low trees. I wither the watered tree and I cause the dried tree to bloom. I am Yahweh, I have declared that this will happen; and I have done it.'”