< Ezekiyel 17 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
Son of man, put forth a riddle, and speak a parable to the house of Israel;
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
and say, Thus saith the Lord Jehovah: A great eagle, with great wings, with long feathers, full of plumage, which had divers colors, came to Lebanon, and took the highest branch of a cedar.
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
He cropped off the top of its young twigs, and carried it into a land of traffic; he set it in a city of merchants.
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
He took also one of the shoots of the land, and put it in a fruitful field; he placed it by great waters, and set it as a willow-tree.
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
And it grew and became a spreading vine of low stature, whose branches turned towards him, and whose roots were under him. It became a vine, that brought forth branches, and shot forth boughs.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
There was also another great eagle, with great wings and many feathers; and, behold, this vine bent its roots toward him, and shot forth its branches toward him, that he might water it from the beds where it was planted.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
And yet it was planted in a good soil, by great waters, that it might bring forth branches, and that it might bear fruit, and be a goodly vine.
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Say thou, Thus saith the Lord Jehovah: Shall it prosper? Shall not he pull up its roots, and cut off its fruit, that it wither? In all the leaves of its branching shall it wither; even without a mighty arm, or many people, shall he pluck it up by the roots.
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
Yea, behold, it is planted; but shall it prosper? Shall it not utterly wither, when the east wind toucheth it? It shall wither in the beds where it grew.
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover, the word of Jehovah came to me, saying:
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
Say now to the rebellious house, Know ye not what these things mean? Say, behold, the king of Babylon came to Jerusalem, and took her king and her princes, and led them with him to Babylon,
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
and took one of the king's offspring, and made a covenant with him, and took an oath of him, and the mighty of the land he took away,
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
that the kingdom might be brought low, so as not to lift itself up; that the covenant might be kept, and stand.
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
But he rebelled against him, in sending his ambassadors into Egypt, that they might give him horses and much people. Shall he prosper? Shall he escape that doeth such things? Shall he break the covenant and be delivered?
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
As I live saith the Lord Jehovah, surely in the place where the king dwelleth that made him king, whose oath he despised, and whose covenant he broke, even with him in the midst of Babylon shall he die.
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
Neither shall Pharaoh with his mighty army and great multitude accomplish anything for him in war, when they shall cast up mounds, and build forts to cut off many persons,
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
he hath despised the oath, and broken the covenant; behold, he hath given the hand, and yet done all these things; he shall not escape!
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
Therefore thus saith the Lord Jehovah: As I live, surely mine oath, which he hath despised, and my covenant, which he hath broken, will I recompense upon his own head.
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
And I will spread my net upon him, and he shall be taken in my snare, and I will bring him to Babylon, and will contend with him there for his trespass which he hath committed against me.
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
And all his fugitives with all his hosts shall fall by the sword, and they that remain shall be scattered to all the winds; and ye shall know that I, Jehovah, have spoken it.
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
Thus saith the Lord Jehovah: I also will take from the top of the high cedar, and will get it; and from the highest of its twigs will I crop a tender one, and plant it upon a high and lofty mountain.
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
Upon a high mountain of Israel will I plant it, and it shall bring forth boughs, and bear fruit, and be a goodly cedar; and under it shall dwell birds of every wing; in the shadow of its branches shall they dwell.
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
And all the trees of the field shall know that I, Jehovah, have brought down the high tree, and exalted the low tree; that I have dried up the green tree, and made the dry tree green. I, Jehovah, have spoken, and will do it.

< Ezekiyel 17 >