< Ezekiyel 16 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
“İnsanoğlu, Yeruşalim'e yaptığı iğrenç uygulamaları bildir.
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
De ki, ‘Egemen RAB Yeruşalim'e şöyle diyor: Kökenin ve doğumun açısından Kenan ülkesindensin; baban Amorlu, annense Hititli'ydi.
4 A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
Doğduğun gün göbek bağın kesilmedi, temizlemek için seni yıkamadılar, tuzla ovalamadılar, kundağa sarmadılar.
5 Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
Kimse bunlardan birini yapacak kadar sana acımadı, sevecenlik göstermedi. Senden tiksindikleri için doğduğun gün seni kıra attılar.
6 “‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
“‘Yanından geçtim, senin kendi kanının içinde kımıldadığını gördüm. Kendi kanının içindeyken yaşa! dedim. Evet, Kendi kanının içindeyken yaşa! dedim.
7 Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
Kırda yetişen bir bitki gibi seni geliştirdim. Geliştin, büyüdün, kusursuz bir güzelliğe eriştin. Göğüslerin oluştu, saçların uzadı. Ama çırılçıplaktın.
8 “‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
“‘Yine yanından geçtim, sana baktım, sevgi çağındı. Giysimin eteğini üzerine serdim, çıplaklığını örttüm. Sana ant içtim, seninle antlaşma yaptım. Egemen RAB böyle diyor. Ve benim oldun.
9 “‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
“‘Seni yıkadım, üzerindeki kanı temizledim, derine zeytinyağı sürdüm.
10 Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
Sana işlemeli giysiler giydirdim, deriden çarık verdim. Beline ince keten kuşak bağladım, seni pahalı giysilerle örttüm,
11 Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
takılarla süsledim. Bileklerine bilezikler, boynuna gerdanlık taktım.
12 na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
Burnuna halka, kulaklarına küpeler, başına görkemli bir taç taktım.
13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
Altınla gümüşle süslendin; giysilerin ince ketenden, pahalı, işlemeli kumaştandı. İnce unla, balla, zeytinyağıyla beslendin. Gitgide güzelleştin, krallığa yaraştın.
14 Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Güzelliğinden ötürü ünün uluslar arasında yayıldı. Çünkü seni görkemimle donattığım için güzelliğin kusursuzdu. Egemen RAB böyle diyor.
15 “‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
“‘Ama sen güzelliğine güvendin, ününü kullanarak fahişelik ettin. Her geçene gönlünü kaptırdın, kendini teslim ettin.
16 Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
Giysilerinden alıp kendine süslü tapınma yerleri yaptın, oralarda fahişelik ettin. Böylesi ne olmuştur, ne de olacaktır.
17 Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
Sana verdiğim altın, gümüş süslerden erkek suretleri yaptın, onlarla fahişelik ettin.
18 Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
İşlemeli giysilerini alıp onların üzerine örttün. Onlara zeytinyağımı, buhurumu sundun.
19 Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Yemen için sağladığım yiyeceği –ince unu, zeytinyağını, balı– güzel kokulu bir sunu olarak onlara sundun. Böyle yaptın diyor Egemen RAB.
20 “‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
“‘Bana doğurduğun oğulları, kızları alıp yiyecek olarak putlara kurban ettin. Fahişelik etmen yetmiyormuş gibi,
21 Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
çocuklarımı kesip sunu olarak ateşte putlara kurban ettin.
22 Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
Bütün iğrenç uygulamalarını, fahişeliklerini yaparken gençlik günlerini, çırılçıplak olduğun, kanının içinde kımıldandığın zamanı anımsamadın.
23 “‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
“‘Egemen RAB, vay, vay başına diyor! Yaptığın kötülüklere ek olarak,
24 kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
kendine fuhuş yuvaları kurdun, bütün meydanlarda yüksek tapınma yerleri yaptın.
25 A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
Her yolun başına kendin için yüksek tapınma yerleri kurdun, güzelliğini kirlettin, her geçene kendini teslim ettin, fahişeliklerini artırdın.
26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
Şehvet düşkünü komşuların Mısırlılar'la fahişelik ettin. Fahişeliklerini artırmakla beni öfkelendirdin.
27 Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
İşte bu yüzden elimi sana karşı uzattım, yiyecek payını azalttım. Ahlaksız davranışından utanç duyan düşmanların Filist kızları dilediklerini yapsınlar diye seni onlara teslim ettim.
28 Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
Asurlular'la da fahişelik ettin, çünkü doymamıştın. Evet, onlarla fahişelik ettin, yine doymadın.
29 Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
Fahişeliğini ticaret diyarı olan Kildan ülkesine dek artırdın, yine de doymadın.
30 “‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
“‘Bütün bunları yaparken yüreğin ne kadar yıpranmış’ diyor Egemen RAB, ‘Yüzsüz bir fahişe gibi davrandın!
31 Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
Her yolun başına fuhuş yuvaları kurarken, bütün meydanlarda yüksek tapınma yerleri yaparken, fahişe gibi bile değildin, ücretini küçümsedin.
32 “‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
“‘Kocasının yerine yabancıları yeğleyen, zina eden bir kadındın!
33 Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
Fahişelere ücret ödenir. Oysa sen bütün oynaşlarına armağanlar dağıttın. Fahişelik etmek için her yandan sana gelsinler diye rüşvet verdin.
34 Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
Fahişeliğinde öbür kadınlara benzemiyorsun. Çünkü fahişelik edesin diye kimse senin peşine düşmüyor. Ücret ödeyen sensin, kimse sana ücret ödemiyor. Bu yüzden öbürlerine benzemiyorsun.
35 “‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
“‘Bu nedenle, ey fahişe, RAB'bin sözünü dinle!
36 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
Egemen RAB şöyle diyor: Yüzsüzlüğün ortaya döküldüğü, oynaşlarınla fahişelik ederken çıplaklığın meydana çıktığı için, bütün iğrenç putların yüzünden, onlara çocuklarının kanını verdiğin için,
37 saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
düşüp kalktığın bütün oynaşlarını –sevdiklerini de nefret ettiklerini de– toplayacağım. Sana karşı onları her yandan toplayacak, çıplaklığını onların önüne sereceğim; bütün çıplaklığını görecekler.
38 Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
Sana zina eden, kan döken kadınlara verilen cezayı vereceğim. Kanını akıtarak seni öfkemin ve kıskançlığımın öcüne terk edeceğim.
39 Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
Seni oynaşlarının eline teslim edeceğim. Fuhuş yuvalarını yıkacak, yüksek tapınma yerlerini bozacaklar. Üzerindeki giysileri soyacak, güzel mücevherlerini alıp seni çırılçıplak bırakacaklar.
40 Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
Halkı sana karşı kışkırtacaklar. Seni taşlayacak, kılıçlarıyla delik deşik edecekler.
41 Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
Evlerini ateşe verecek, seni birçok kadının gözü önünde yargılayacaklar. Fahişeliklerine son vereceğim, artık oynaşlarına ücret ödemeyeceksin.
42 Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
Böylece sana karşı öfkem yatışacak, kıskançlığım dinecek. Susacak, bir daha öfkelenmeyeceğim.
43 “‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
“‘Madem gençlik günlerini anımsamadın, yaptıklarınla beni öfkelendirdin, ben de yaptıklarını senin başına getireceğim. Böyle diyor Egemen RAB. Bu iğrenç uygulamalarına ek olarak ahlaksızlık da ettin.
44 “‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
“‘Herkes senin için şu deyişi söyleyecek: Annesi nasılsa kızı da öyle.
45 Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
Sen kocasından ve çocuklarından tiksinen annenin kızısın; kocalarından ve çocuklarından tiksinen kızkardeşlerinin kızkardeşisin. Annen Hititli, baban Amorlu'ydu.
46 Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
Kızlarıyla senin kuzeyinde yaşayan Samiriye ablan, kızlarıyla senin güneyinde yaşayan Sodom kızkardeşindir.
47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
Sen yalnız onların yolunda yürümekle, onların iğrenç uygulamalarına uymakla kalmadın, bütün yaptıklarınla kısa sürede onlardan daha büyük kötülük ettin.
48 Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
Varlığım hakkı için diyor Egemen RAB, kızkardeşin Sodom'la kızları, kızlarınla senin yaptıklarını asla yapmadılar.
49 “‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
“‘Kızkardeşin Sodom'un günahı şuydu: Kendisi de kızları da gururluydu, ekmeğe doymuşlardı, umursamazlardı. Düşküne, yoksula yardım elini uzatmadılar.
50 Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
Kendilerini beğenmişlerdi. Önümde iğrenç şeyler yaptılar. Bu nedenle, gördüğün gibi onları önümden süpürüp attım.
51 Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
Samiriye işlediğin günahın yarısını bile işlemedi. Sen onlardan çok daha iğrenç şeyler yaptın. Yaptığın iğrençliklerle kızkardeşlerini suçsuz çıkardın.
52 Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
Düşeceğin utanca katlanacaksın. Çünkü kızkardeşlerini haklı gibi gösterdin. İşlediğin günahlar onlarınkinden daha iğrenç olduğundan senin yanında suçsuz kalıyorlar. Bunun için utan ve düşeceğin utanca katlan. Çünkü kızkardeşlerini suçsuz çıkardın!
53 “‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
“‘Sodom'la kızlarını, Samiriye'yle kızlarını, onlarla birlikte de seni eski gönencine kavuşturacağım.
54 domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
Utanca boğulacaksın. Bütün yaptıklarından ötürü kızkardeşlerine avuntu olacak ve utanacaksın.
55 ’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
Kızkardeşlerin Sodom ve Samiriye ile kızları eski durumlarına dönecekler; kızlarınla sen de öyle.
56 Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
Kötülüğün açığa çıkmadan önce, gururlu olduğun günlerde kızkardeşin Sodom'un adını bile anmıyordun. Şimdi sen de Edom kızlarıyla komşuları ve Filist kızlarınca –çevrende seninle alay edenlerce– küçümseniyorsun.
57 kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
Ahlaksızlığının ve yaptığın iğrençliklerin sonuçlarına katlanacaksın. RAB böyle diyor.
59 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
“‘Egemen RAB şöyle diyor: Seninle yaptığım antlaşmayı bozarak içtiğin andı küçümsedin. Ben de hak ettiğin biçimde seni cezalandıracağım.
60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
Gençlik günlerinde seninle yaptığım antlaşmayı anımsayacağım. Seninle sonsuza dek kalıcı bir antlaşma yapacağım.
61 Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
Büyük, küçük kızkardeşlerini yanına aldığında yaptıklarını anımsayacak ve utanacaksın. Seninle yaptığım antlaşmada olmadığı halde onları kızların olsunlar diye sana vereceğim.
62 Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
Seninle yeniden antlaşma yapacağım, benim RAB olduğumu anlayacaksın.
63 Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Bütün yaptıklarını bağışladığımda, anımsayacak ve utanacaksın. Utancından bir daha ağzını açmayacaksın. Egemen RAB böyle diyor.’”