< Ezekiyel 16 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
LEUM GOD El sifil kaskas nu sik,
2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
ac fahk, “Mwet sukawil moul la, fahkang nu sin Jerusalem orekma srungayuk ma el orala.
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
Fahk nu sin Jerusalem ma LEUM GOD Fulatlana El fahk nu sel: “Kom tuh isusla in facl sin mwet Canaan. Papa tomom el sie mwet Amor ac nina kiom el sie mwet Hit.
4 A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
Ke pacl se kom isusla ah, wangin mwet lusala futom, ku twetekinkomla, ku sohlela monum, ku pwikomla ke ipin nuknuk.
5 Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
Wangin mwet pakomutom in oru kutu sin ma inge nu sum. Ke kom isusla ah, sisila kom nu inima ke sripen wangin mwet lungse kom.
6 “‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
“Na nga fahsryak ac liye ke kom oan tipirpir in srah keim an. Monum afla ke srah, tusruktu nga tia lela kom in misa.
7 Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
Nga tufwe kom in kapak oana soko sacn ma kapak wo. Kom kapak kui ac mutan fusrla. Wo aten titi lom, loes aunsifom, tusruktu kom koflufol.
8 “‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
“Ke nga sifil fahsryak insac, nga liye lah kom nunak in payuk. Na nga afinya monum ke nuknuk lik luk, ac wuleot mu nga ac lungse kom. Aok, nga orala sie wuleang in marut inmasrloktal, na kom ma lac luk.” Pa inge ma LEUM GOD Fulatlana El fahk.
9 “‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
“Na nga otema kutu kof ac twanla srah keim, ac nga sang oil in olive mosrwekomla.
10 Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
Nga nukumkomyang ke nuknuk orekla ke mwe akul na kato, ac sot fahluk orek ke kulun kosro na wowo, ac nga sot sie nuknuk linen mwe lohl suf, ac sie nuknuk lik orekla ke silk.
11 Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
Nga nawekomla ke mwe lohlpo, ac ah nu inkwawom ma orekla ke eot saok.
12 na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
Nga sot sie ring nu ke fwem, oayapa yaring, ac sie tefuro na oasku.
13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
Oasr mwe naweyuk lom orekla ke gold ac silver, ac pacl nukewa kom nukum nuknuk linen ac silk ma akul uh. Kom mongo bread ma orekla ke flao wowo, ac oasr honey ac oil in olive kom kang. Katoiyom arulana oasku, na kom kasrala.
14 Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Kom pwengpeng in mutunfacl nukewa ke sripen kato lom, mweyen nga pa orekomla in arulana oasku.” Pa inge ma LEUM GOD Fulatlana El fahk.
15 “‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
“Tuh ke sripen kom konkun kato ac pwengpeng lom, kom oan yurin kutena mukul su tuku nu yurum.
16 Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
Kom orekmakin kutu nuknuk lom in sang yuni nien alu sum. Na kom eiskomyang nu sin kutena mukul, oana sie mutan kosro su eis molin kosro lal.
17 Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
Kom eisla mwe yun silver ac gold su nga sot lom, ac kom sang taflela ma sruloala in luman mukul uh, ac orek kosro nu kac.
18 Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
Kom eisla nuknuk akul su nga sot lom ac sang nokomang ma sruloala ingan, ac kom kisakin nu selos oil in olive ac mwe keng ma nga sot nu sum.
19 Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Nga sot nom flao na wowo, oil in olive, ac honey, tuh pa kom kisakin ma inge in akinsewowoye ma sruloala uh.” Pa inge ma LEUM GOD Fulatlana El fahk.
20 “‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
“Na kom eis tulik mukul ac mutan ma kom oswela nu sik, ac kisakunulos nu ke ma sruloala uh. Ya tia fal tari ke kom tia pwaye nu sik?
21 Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
Na efu kom ku sifil sang tulik nutik uh in mwe kisa nu ke ma sruloala?
22 Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
Ke pacl se kom moulkin lumah srungayuk oana sie mutan kosro, kom tiana esamak pacl se kom tulik, koflufol ac tipirpir in srah keim sifacna.”
23 “‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
LEUM GOD Fulatlana El fahk, “We nu sum! Kom oru ma koluk inge nukewa,
24 kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
na sisken inkanek nukewa kom musaela nien alu nu ke ma sruloala, ac iwen orek kosro.
25 A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
Kom akfohkfokyela kato lom yen furarrar, ac kom fuhleang monum nu sin kutena mukul su fahsryak, ac moul in kosro lom uh yokelik len na len.
26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
Kom kukakin monum nu sin mwet Egypt, su mwet tulan elahn kosro, na kom oru kosro lom uh in akkasrkusrakyeyu.
27 Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
“Na inge, nga srukak pouk in kai kom, ac in eisla ip lom ke mwe insewowo luk uh. Nga eiskomyang nu inpoun mwet Philistia su srungakom ac mwekin ke moul fohkfok lom.
28 Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
“Ke sripen kom tiana muti yorolos, oru kom ukwe mwet Assyria. Kom kukakin monum nu selos, tuh kom tia pac muti selos.
29 Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
Kom oayapa orek kosro yurin mwet Babylonia, sie facl pwengpeng ke kuka, tuh pa kom tia pac muti selos.”
30 “‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
Pa inge ma LEUM GOD Fulatlana El fahk: “Kom oru ma inge nukewa oana sie mutan kosro na sumwekin.
31 Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
Kom musaela acn in alu nu ke ma sruloala oayapa iwen orek kosro ke inkanek nukewa. Tusruktu kom tia sukok mani in oana mutan saya ma kukakin manolos.
32 “‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
Kom oana mutan su lungse orek kosro yurin mukul saya, ac tia lungse oan yurin mukul tumal sifacna.
33 Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
Mutan kosro uh elos eis molin kosro lalos, a kom sang monum, tia moul, nu sin mukul ma orek pwar nu sum, ac kom sang mani in eyeinse nu selos in tuku liki acn nukewa ac oan yurum.
34 Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
Kom tiana oana mutan kosro saya. Wangin mwet akkohsye kom in sie mutan kosro. Tia moul nu sum, a kom moli nu selos! Pwayena lah kom siena lukelos.”
35 “‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
Jerusalem, kom mutan kosro se! Inge, lohng ma LEUM GOD El fahk uh.
36 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
Pa inge ma LEUM GOD Fulatlana El fahk: “Kom tuh sarukla nuknuk lom, na oana sie mutan kosro kom tuh eiskomyang sifacna nu sin mukul kawuk lom ac nu ke ma sruloala srungayuk nukewa lom. Ac kom oayapa uniya tulik nutum ac kisakunulos nu ke ma sruloala uh.
37 saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
Ke sripa inge, nga ac eisani nufon mwet kom orek pwar nu se meet ah — elos su kom lungse ac elos su kom srunga. Nga ac usalosme elos in raunikomla, na nga ac sarukkomla ac sang elos in liye ke kom koflufol uh.
38 Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
Nga ac nununkekom ke sripen kom kunausla wulela in marut lom, ac oayapa akmas. In kasrkusrak lulap luk, nga wotela mu kom ac misa.
39 Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
Nga ac filikomi ye ku lalos, ac elos ac kunausya acn kom orekmakin in kukakin monum, ac nien alu lom nu ke ma sruloala. Elos ac usla nuknuk lom ac mwe yun lom, ac filikomi koflufol.
40 Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
“Elos ac purakak sie un mwet in tungal kom nwe ke kom misa, ac elos ac sipsipikya monum nu ke ip srisrik ke cutlass natulos.
41 Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
Elos ac esukak lohm sum nukewa, ac oru tuh mutan puspis in liye kaiyuk nu sum uh. Nga ac oru kom in tui liki moul in kosro lom an, ac oru kom in tia sifil sang mwe moul nu sin mukul kom orek pwar yoro.
42 Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
Ouinge kasrkusrak luk ac safla, ac nga fah inse misla. Nga fah tia sifil kasrkusrak, ac tia sifilpa lemta.
43 “‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
Kom mulkunla orekma luk nu sum ke kom srik ah, ac kom akkasrkusrakyeyu ke ma nukewa kom orala. Ouinge nga ac oru kom in eis mwatan ma inge nukewa. Efu kom ku sang elahn kosro in weang ma srungayuk nukewa ma kom orala?” LEUM GOD Fulatlana pa fahk ma inge.
44 “‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
LEUM GOD El fahk, “Jerusalem, mwet uh ac fahk soakas se inge keim: ‘Tulik mutan se ac kwa nina kial.’
45 Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
Pwayena lah kom kwa nina kiom uh. El arulana srunga mukul tumal ac tulik natul. Kom oana tamtael wiom su srunga mukul tumalos ac tulik natulos. Kom, ac siti wiom ingan, ma nutin nina Hit se ac papa Amor se.
46 Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
“Mutan se wiom ma matu pa Samaria layen epang, wi inkul ma oan raunela. Ac mutan se wiom ma fusr pa Sodom layen eir, wi inkul ma oan raunela.
47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
Ku kom falkin in fahsr in falkalos ac etai ouiya srungayuk elos oru? Mo. In kitin pacl ah na kom orekma koluk yohk lukelos in ma nukewa kom oru.”
48 Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
LEUM GOD Fulatlana El fahk, “Oana ke nga pa God moul, Sodom mutan se wiom ac inkul ma raunela, tiana oru ouiya koluk ma kom, ac inkul raunikomla ingan, orala.
49 “‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
El, ac acn natul uh, arulana konkin ke pus mwe mongo nalos ac elos muta in misla ac insraelak, tusruktu elos tiana kasru mwet sugasrup ac mwet enenu.
50 Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
Elos inse fulat ac likkeke ac oru ma nga srunga, pwanang nga kunauselosla, oana kom etu.
51 Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
“Ma koluk lal Samaria tia tafu nu ke ma koluk kom orala. Kom oru ma srungayuk arulana yohk liki ma el orala. Ouiya srungayuk lom uh arulana yohk, oru oana in wangin ma koluk lun mutan luo wiom kut fin kapsra ma koluk lalos nu ke ma koluk lom uh.
52 Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
Inge mwekin lom uh ac fah oanna fom. Moul koluk lom an arulana yohk liki mutan luo wiom, pwanang mwet uh pangon mu wangin ma koluk lalos. Kom ac mwekyekinna, mweyen ma koluk lom uh oru oana in wangin mwatan mutan luo wiom.”
53 “‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
LEUM GOD El fahk nu sin Jerusalem, “Nga ac oru tuh Sodom ac inkul we, oayapa Samaria ac inkul we, in sifil kapkapak. Aok, nga ac oru tuh kom in kapkapak pac.
54 domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
Kom ac mwekyekin orekma koluk lom an, na mwekin lom uh ac oru mutan wiom an in akilen lah ma koluk lalos uh srik liki kom.
55 ’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
Elos ac sifilpa akwoyeyuk oana meet, na kom, ac inkul lom, ac sifil akwoyeyukla pac.
56 Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
Ya kom tuh tia orek aksruksruk ke acn Sodom in pacl kom inse fulat,
57 kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
meet liki ma koluk lom fwackyak? Inge kom oapana el, sie mwe aksruksruk yurin mwet Edom, mwet Philistia, ac mutunfacl atulani lom su srungakom.
58 Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
Kom ac fah keok ke ouiya fohkfok ac srungayuk ma kom orala.” LEUM GOD pa fahk ma inge.
59 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
LEUM GOD Fulatlana El fahk, “Nga fah oru nu sum fal nu ke orekma lom, mweyen kom pilesru wulela lom ac kunausla wuleang inmasrlosr.
60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
Tusruktu nga fah esam na wuleang su nga orala nu sum ke kom srakna fusr, ac nga fah oakiya yurum sie wuleang su ac fah oan nwe tok.
61 Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
Kom ac esam ouiyen moul lom ac mwekin kac ke kom ac sifil eis tamtael matu ac fusr wiom. Nga fah eisaloswot tuh elos in oana acn nutum, finne tia ipin wuleang se ma nga orala yurum ah.
62 Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
Nga ac aksasuyela wuleang luk yurum, ac kom fah etu lah nga pa LEUM GOD.
63 Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Nga fah nunak munas ke ma koluk nukewa ma kom orala, tusruktu kom fah esam na ma ingan ac mwekin in fahk kutena ma.” LEUM GOD Fulatlana pa fahk ma inge.