< Ezekiyel 16 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
O son of humankind make known to Jerusalem abominations its.
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
And you will say thus he says [the] Lord Yahweh to Jerusalem origins your and birth your [were] from [the] land of the Canaanite[s] father your [was] Amorite and mother your [was] a Hittite.
4 A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
And birth your on [the] day were born you not it was cut off umbilical cord your and with water not you were washed for cleansing and certainly not you were rubbed with salt and certainly not you were wrapped.
5 Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
Not it looked with compassion on you an eye to do for you one of these [things] for compassion on you and you were thrown out to [the] surface of the field in [the] loathing of life your on [the] day were born you.
6 “‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
And I passed by at you and I saw you kicking about in blood your and I said to you in blood your live and I said to you in blood your live.
7 Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
Ten thousand like [the] growth of the field I made you and you grew and you grew up and you came into adornment ornaments breasts they were firm and hair your it had grown and you [were] nakedness and bareness.
8 “‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And I passed by at you and I saw you and there! time your [was] a time of love and I spread out [the] skirt of garment my over you and I covered nakedness your and I swore an oath to you and I came in a covenant with you [the] utterance of [the] Lord Yahweh and you belonged to me.
9 “‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
And I washed you with water and I washed off blood your from on you and I anointed you with oil.
10 Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
And I clothed you multicolored cloth and I shod you leather and I wrapped head your with fine linen and I covered you silk.
11 Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
And I ornamented you ornament[s] and I put! bracelets on hands your and a chain on neck your.
12 na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
And I put a ring on nose your and earrings on ears your and a crown of beauty on head your.
13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
And you ornamented yourself gold and silver and clothing your ([was] fine linen *Q(K)*) and silk and multicolored cloth fine flour and honey and oil (you ate *Q(k)*) and you were beautiful with muchness muchness and you prospered into kingship.
14 Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And it went out of you name among the nations on beauty your for - [was] perfect it on splendor my which I had put on you [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
15 “‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
And you trusted in beauty your and you acted as a prostitute on name your and you poured out prostitution your on every [one who] passed by to him let it belong.
16 Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
And you took some of clothes your and you made for yourself high places multicolored and you acted as a prostitute on them not coming and not it will be.
17 Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
And you took [the] articles of beauty your some of gold my and some of silver my which I had given to you and you made for yourself images of a male and you acted as a prostitute with them.
18 Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
And you took [the] clothes of multicolored cloth your and you covered them and oil my and incense my (you put *Q(k)*) before them.
19 Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And food my which I had given to you fine flour and oil and honey [which] I had given to eat you and you put it before them to an odor of soothing and it was [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
20 “‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
And you took sons your and daughters your whom you had borne to me and you sacrificed them to them to devour ¿ little (from prostitution your. *Q(K)*)
21 Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
And you slaughtered children my and you gave them when made pass through them to them.
22 Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
And with all abominations your and prostitution your not (you remembered *Q(k)*) [the] days of youth your when were you nakedness and bareness kicking about in blood your you were.
23 “‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
And it was after all wickedness your woe! woe! to you [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
24 kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
And you built for yourself a mound and you made for yourself a high place in every open place.
25 A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
To every head of a road you built high place your and you made abominable beauty your and you opened wide feet your for every [one who] passed by and you increased (prostitution your. *Q(K)*)
26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
And you acted as a prostitute to [the] people of Egypt neighbors your becoming great of flesh and you increased prostitution your to provoke to anger me.
27 Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
And there! I stretched out hand my on you and I diminished allotment your and I gave you in [the] will of [those who] hate you [the] daughters of [the] Philistines who were ashamed from conduct your licentiousness.
28 Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
And you acted as a prostitute to [the] people of Assyria from not satiety your and you acted as a prostitute with them and also not you were satisfied.
29 Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
And you increased prostitution your to a land of merchant[s] Chaldea towards and also by this not you were satisfied.
30 “‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
How! hot [is] anger your [the] utterance of [the] Lord Yahweh when do you all these [things] [the] deed[s] of a woman a prostitute imperious.
31 Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
When built you mound your at [the] head of every road and high place your (you made *Q(k)*) in every open place and not (you were *Q(k)*) like prostitute to scorn [the] hire of a prostitute.
32 “‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
O wife adulterous [who] in place of husband her she takes strangers.
33 Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
To all prostitutes men give a gift and you you have given gift your to all lovers your and you have bribed them to come to you from round about by prostitution your.
34 Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
And it was in you contrariness from the women in prostitution your and after you not it was approached for prostitution and because gave you [the] hire of a prostitute and [the] hire of a prostitute not it was given to you and you became contrariness.
35 “‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
Therefore O prostitute hear [the] word of Yahweh.
36 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
Thus he says [the] Lord Yahweh because was poured out lust your and it was uncovered nakedness your in prostitution your with lovers your and on all [the] idols of abominations your and according to [the] blood of children your which you gave to them.
37 saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
Therefore here I [am] about to gather all lovers your whom you were pleasing to them and all [those] whom you loved to all [those] whom you hated and I will gather them on you from round about and I will uncover nakedness your to them and they will see all nakedness your.
38 Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
And I will judge you judgments of adulteresses and [women who] shed blood and I will put on you blood of rage and jealousy.
39 Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
And I will give you in hand their and they will tear down mound your and they will be broken down high places your and they will strip off you clothes your and they will take [the] articles of beauty your and they will leave you nakedness and bareness.
40 Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
And they will bring up on you a company and they will stone you with stone[s] and they will cut to pieces you with swords their.
41 Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
And they will burn houses your with fire and they will bring about on you judgments to [the] eyes of women many and I will cause to cease you from a prostitute and also [the] hire of a prostitute not you will give again.
42 Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
And I will give rest to rage my on you and it will turn aside jealousy my from you and I will be at peace and not I will be angry again.
43 “‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
Because that not (you remembered *Q(k)*) [the] days of youth your and you were enraged to me in all these [things] and also I there! conduct your - on [the] head I will requite [the] utterance of [the] Lord Yahweh and not (did you do? *Q(k)*) the licentiousness to all abominations your.
44 “‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
There! every [one who] speaks a proverb on you he will speak a proverb saying [is] like mother her daughter her.
45 Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
[are] [the] daughter of Mother your you [who] loathed husband her and children her and [are] [the] sister of sister your you who they loathed husbands their and children their mother your [was] a Hittite and father your [was] an Amorite.
46 Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
And sister your old [was] Samaria she and daughters her who dwelt on north your and sister your young more than you who dwelt from south your [was] Sodom and daughters her.
47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
And not in ways their did you walk? and in abominations their (did you do? *Q(k)*) like a little only and you behaved corruptly more than them in all ways your.
48 Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
[by] [the] life Of me [the] utterance of [the] Lord Yahweh if she did Sodom sister your she and daughters her just as you have done you and daughters your.
49 “‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
Here! this it was [the] iniquity of Sodom sister your pride surfeit of food and ease of quietness it belonged to her and to daughters her and [the] hand of [the] poor and [the] needy not she strengthened.
50 Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
And they were haughty and they did abomination before me and I removed them just when I saw.
51 Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
And Samaria according to [the] half of sins your not it sinned and you have increased abominations your more than them and you have made appear righteous (sisters your *Q(K)*) by all abominations your which (you have done. *Q(k)*)
52 Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
Also you - bear disgrace your that you have mediated for sister your by sins your which you have acted abominably more than them they are righteous more than you and also you be ashamed and bear disgrace your because have made appear righteous you sisters your.
53 “‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
And I will turn back captivity their ([the] captivity of *Q(k)*) Sodom and daughters her and ([the] captivity of *Q(k)*) Samaria and daughters her (and [the] captivity of *Q(k)*) captivities your in midst of them.
54 domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
So that you may bear disgrace your and you will be ashamed from all that you have done when comfort you them.
55 ’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
And sisters your Sodom and daughters her they will return to former state their and Samaria and daughters her they will return to former state their and you and daughters your you will return to former state your.
56 Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
And not did she become? Sodom sister your a mention in mouth your in [the] day of pride your.
57 kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
Before it was uncovered wickedness your like [the] time of [the] reproach of [the] daughters of Aram and all around it [the] daughters of [the] Philistines who despise you from round about.
58 Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
Licentiousness your and abominations your you you will bear them [the] utterance of Yahweh.
59 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
That thus he says [the] Lord Yahweh (and I will deal with *Q(K)*) with you just as you have done [you] who you despised an oath by breaking a covenant.
60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
And I will remember I covenant my with you in [the] days of youth your and I will establish for you a covenant of perpetuity.
61 Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
And you will remember ways your and you will be ashamed when receive you sisters your old more than you to young more than you and I will give them to you to daughters and not from covenant your.
62 Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
And I will establish I covenant my with you and you will know that I [am] Yahweh.
63 Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
So that you may remember and you will be ashamed and not it will belong to you again an opening of a mouth because of disgrace your when make atonement I for you for all that you have done [the] utterance of [the] Lord Yahweh.

< Ezekiyel 16 >