< Ezekiyel 16 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
Son of man, cause Jerusalem to know her abominations,
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
and say, Thus saith the Lord Jehovah to Jerusalem: Thine origin and thy nativity were of the land of Canaan. Thy father was an Amorite, and thy mother a Hittite.
4 A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
And as to thy nativity, in the day thou wast born thy navel was not cut, neither wast thou washed in water so as to be cleansed. Thou wast not sprinkled with salt, nor wrapped in swaddling-clothes.
5 Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
No eye pitied thee, to do to thee any of these things, to have compassion upon thee; but thou wast cast out into the open field, so as to loathe thyself, on the day thou wast born.
6 “‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
And when I passed by thee, and saw thee in danger of being trodden under foot in thy blood, I said to thee when thou wast in thy blood, Live! yea, I said to thee when thou wast in thy blood, Live!
7 Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
I caused thee to increase like the plant of the field, and thou didst grow, and become tall, and didst attain to distinguished charms. Thy breasts swelled, and thy hair grew, whereas thou wast naked and bare.
8 “‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And when I passed by thee, and saw thee, behold, it was thy time, the time of love. And I spread my skirt over thee and covered thy nakedness; and I swore to thee, and entered into covenant with thee, and thou becamest mine.
9 “‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
Then I washed thee with water, yea, I thoroughly washed away thy blood from thee, and I anointed thee with oil.
10 Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
I clothed thee also with broidered work, and gave thee shoes of seal's skin, and wrapped thee about with fine linen, and covered thee with silk.
11 Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
And I decked thee with ornaments, and put bracelets upon thy hands, and a chain upon thy neck.
12 na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
And I put a jewel in thy nostril, and ear-rings in thine ears, and a beautiful crown upon thy head.
13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
Thus wast thou adorned with gold and silver, and thy raiment was of fine linen, and silk, and broidered work. Fine flour and honey and oil didst thou eat; and thou wast exceedingly beautiful, and didst prosper so as to become a queen.
14 Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And thy renown went forth among the nations for thy beauty; for it was perfect through my comeliness, which I had put upon thee, saith the Lord Jehovah.
15 “‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
But thou didst trust in thy beauty, and didst play the harlot because of thy renown, and didst lavish thy fornications on every one that passed by; his was it.
16 Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
And of thy garments thou didst take, and didst make thee high places, spread with divers colors, and didst play the harlot thereon, the like things to which shall not come to pass, neither shall they be.
17 Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
Thou didst take also thy fair jewels of my gold and my silver, which I gave thee, and didst make to thyself images of men, and didst commit fornication with them;
18 Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
and thou didst take thy broidered garments and cover them; and thou didst set mine oil and mine incense before them.
19 Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
My food also, which I gave thee, fine flour and oil and honey, wherewith I fed thee, thou didst set it before them with a sweet savor; even thus it was, saith the Lord Jehovah.
20 “‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
Moreover thou didst take thy sons and thy daughters, whom thou didst bear to me, and these didst thou sacrifice to them to be devoured. Was it not enough for thee to commit fornication,
21 Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
that thou didst slay my children, and deliver them up to cause them to pass through the fire to them?
22 Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
And in all thine abominations and thy fornications, thou didst not remember the days of thy youth, when thou wast naked and bare, and in danger of being trampled under foot in thy blood.
23 “‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
And it came to pass, after all thy wickedness, (woe, woe to thee! saith the Lord Jehovah, )
24 kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
that thou didst build for thee an arched place, and make thee a high place in every street;
25 A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
at every head of the way didst thou build thy high place, and didst make thy beauty to be abhorred, and didst open thy feet to every one that passed by, and didst multiply thy fornications.
26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
Thou hast also committed fornication with the Egyptians, thy neighbors, having great members, and hast multiplied thy fornications to provoke me to anger.
27 Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
Therefore, behold, I have stretched out my hand against thee, and have diminished thine allowance, and delivered thee to the will of them that hate thee, the daughters of the Philistines, who are ashamed of thy lewd way.
28 Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
Thou hast also committed fornication with the Assyrians, because thou wast insatiable; yea, thou hast played the harlot with them, and yet couldst not be satisfied.
29 Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
Thou hast also multiplied thy fornication with the land of Canaan, even to Chaldaea; and yet wast thou not satisfied therewith.
30 “‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
How faint was thy heart, saith the Lord Jehovah, that thou didst all those things which an imperious whorish wife doeth,
31 Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
in that thou didst build thine arched place at the head of every way, and make thy high place in every street! Thou wast not like a harlot, who scoffeth at her hire,
32 “‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
but as an adulterous wife, that taketh strangers instead of her husband.
33 Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
To all women that commit fornication men give a reward; but thou gavest thy gifts to all thy lovers, and hiredst them to come to thee from every side to commit fornication with thee.
34 Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
Thou wast the reverse of other women in thy fornications. None followed after thee to commit fornication, but thou gavest the reward, and no reward was given thee, —therefore thou wast the reverse.
35 “‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
Wherefore, O harlot, hear the word of Jehovah!
36 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
Thus saith the Lord Jehovah: Because thy treasure was poured out, and thy nakedness discovered for fornication before thy lovers, and all thine abominable idols, and because of the blood of thy children, which thou didst give to them,
37 saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
therefore, behold, I will gather all thy lovers, to whom thou wast pleasing, all them that thou hast loved, with all them that thou hast hated, I will gather them against thee round about, and will uncover thy nakedness to them, that they may see all thy nakedness.
38 Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
And I will judge thee as women that break wedlock and shed blood are judged, and I will cause thy blood to flow in fury and jealousy.
39 Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
And I will give thee into their hand, and they shall throw down thine arched place, and break down thy high places. They shall also strip thee of thy clothes, and leave thee naked and bare.
40 Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
They shall also bring up a company against thee, and they shall stone thee with stones, and thrust thee through with their swords;
41 Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
and they shall burn thine houses with fire, and execute judgments upon thee in the sight of many women; and I will cause thee to cease from playing the harlot, and thou shalt give hire no more.
42 Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
So will I make my fury toward thee to rest, and my jealousy shall depart from thee; and I will be quiet, and will be no more angry.
43 “‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
Because thou hast not remembered the days of thy youth, but hast raged against me in all these things, therefore I also will recompense thy way upon thy head, saith the Lord Jehovah, so that thou shalt not commit this wickedness in addition to all thy abominations.
44 “‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
Behold, all they that use proverbs shall utter this proverb concerning thee: “As the mother, so the daughter.”
45 Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
Thou art the daughter of thy mother, that loathed her husband and her children; and thou art the sister of thy sisters, that loathed their husbands and their children; your mother was a Hittite, and your father an Amorite.
46 Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
And thine elder sister is Samaria, with her daughters, that dwelleth at thy left hand; and thy younger sister, that dwelleth at thy right hand, is Sodom, with her daughters.
47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
Yet thou hast not walked in their ways, nor done according to their abominations: that was disdained by you, as a very little thing; thou hast been more corrupt than they in all thy ways.
48 Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
As I live, saith the Lord Jehovah, Sodom, thy sister, hath not done, she nor her daughters, as thou hast done, thou and thy daughters.
49 “‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
Behold, this was the iniquity of Sodom, thy sister: in pride, superabundance, and careless ease did she live, she and her daughters, and the hand of the poor and needy she did not strengthen;
50 Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
and they were haughty, and committed abomination before me; therefore I took them away when I saw it.
51 Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
Neither hath Samaria committed half of thy sins; but thou hast multiplied thine abominations more than they, and hast justified thy sisters in all thine abominations which thou hast done.
52 Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
Now, therefore, bear thou thy shame, to which thou hast condemned thy sisters, since by thy sins which thou hast committed, more abominable than they, they are more righteous than thou. Yea, be thou confounded and bear thy shame, in that thou hast justified thy sisters.
53 “‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
Yet I will bring them back from their captivity, even Sodom and her daughters from their captivity, and Samaria and her daughters from their captivity; thee also will I bring back from thy captivity in the midst of them;
54 domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
that thou mayst bear thy shame, and mayst be confounded on account of all which thou hast done, in that thou art a comfort to them.
55 ’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
And thy sisters, Sodom and her daughters, shall return to their former estate, and Samaria and her daughters shall return to their former estate, and thou and thy daughters shall return to your former estate.
56 Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
And yet Sodom, thy sister, was not mentioned by thy mouth in the day of thy pride
57 kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
before thy wickedness was discovered, as in the time of thy reproach from the daughters of Syria, and from all that were round about her, and from the daughters of the Philistines, who despised thee round about.
58 Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
Thy wickedness and thine abominations must thou now bear, saith the Lord Jehovah.
59 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
For thus saith the Lord Jehovah: I will do to thee as thou hast done, who hast despised the oath and hast broken the covenant.
60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
But I will remember my covenant with thee in the days of thy youth, and I will establish with thee an everlasting covenant.
61 Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
Then shalt thou remember thy ways, and be ashamed, when thou shalt receive thy sisters, thine elder and thy younger, and I shall give them to thee for daughters, but not by thy observance of thy covenant.
62 Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
But I will establish my covenant with thee, and thou shalt know that I am Jehovah;
63 Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
that thou mayst remember and be confounded, and not open thy mouth any more for shame, when I forgive thee all which thou hast done, saith the Lord Jehovah.

< Ezekiyel 16 >