< Ezekiyel 16 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came unto me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
Son of man, make known unto Jerusalem her abominations,
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
And thou shalt say, Thus hath said the Lord Eternal unto Jerusalem, Thy origin and thy birth are out of the land of Canaan: thy father was an Emorite, and thy mother a Hittite.
4 A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
And as for thy birth, on the day thou wast born thy navel was not cut, nor wast thou washed in water to he cleansed; and thou wast not rubbed with salt, nor wrapt in swaddling clothes.
5 Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
No eye looked with pity on thee, to do any of these things unto thee, to have compassion upon thee; but thou wast cast out on the open field, with a loathing of thy body, on the day that thou wast born.
6 “‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
But I passed then by thee, and I saw thee stained with thy own blood, and I said unto thee, In thy blood, live; yea, I said unto thee, In thy blood, live.
7 Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
Myriads, like the vegetation of the field, did I make of thee, and thou didst increase and become great, and thou attainedst the highest attractions: with thy breasts developed, and thy hair full grown; but thou wast still naked and bare.
8 “‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
But I passed then by thee, and saw thee, and, behold, thy time was the time of love; and I spread the skirt of my garment over thee, and covered thy nakedness: yea, I swore unto thee, and entered into a covenant with thee, saith the Lord Eternal, and thou becamest mine.
9 “‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
Then did I bathe thee with water, yea, I thoroughly washed away thy blood from thee; and I anointed thee with oil.
10 Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
I clothed thee also with broidered work, and made thee shoes of badger's skin, and I placed on thy head a turban of fine linen, and I covered thee with silk.
11 Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
And I decked thee with ornaments, and I placed bracelets upon thy hands, and a chain around thy neck.
12 na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
And I placed a ring on thy nose, and earrings in thy ears, and a crown of splendor on thy head.
13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
Thus wast thou ornamented with gold and silver; and thy garments were of fine linen, and silk, and broidered work; fine flour, and honey, and oil didst thou eat: and thou wast exceedingly beautiful, and thou didst succeed to acquire dominion.
14 Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And thy fame went forth among the nations because of thy beauty; for it was perfect through my glorious ornament, which I had put upon thee, saith the Lord Eternal.
15 “‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
But thou didst trust in thy beauty, and play the harlot because of thy fame, and lavish thy lewd caresses on every one that passed by—on him they were bestowed.
16 Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
And thou didst take from thy garments, and deck thee high-places with divers colors, and play the harlot thereupon: never should the like come to pass, and never should it be so.
17 Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
And thou didst take thy elegant ornaments of my gold and of my silver, which I had given thee, and make for thyself male images, and play the harlot with them;
18 Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
And thou didst take thy broidered garments, and cover them: and my oil and my incense didst thou place before them.
19 Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And my bread which I had given thee, fine flour, and oil, and honey, which I had let thee eat, even this didst thou set before them for a sweet savour: yes, so was it, saith the Lord Eternal.
20 “‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
And thou didst take thy sons and thy daughters, whom thou hadst born unto me, and didst slaughter these unto them to be devoured; [but] were thy acts of lewdness not yet enough?
21 Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
That thou didst slay my children, and give them up to cause them to pass through the fire for them?
22 Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
And in all thy abominations and thy acts of lewdness thou didst not remember the days of thy youth, when thou wast naked and bare, when thou wast stained with thy blood.
23 “‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
And it came to pass after all thy wickedness, —[woe, woe unto thee! saith the Lord Eternal; ]—
24 kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
That thou didst build unto thyself eminences, and make thyself elevations in every street.
25 A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
On the corner of every road didst thou build thy elevations, and make thy beauty abominable, and spread out thy feet to every one that passed by, and multiply thy acts of lewdness.
26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
And thou didst play the harlot with the Egyptians, thy neighbors, with large limbs, and multiply thy acts of lewdness, to provoke me to anger.
27 Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
And, behold, I stretched out my hand over thee, and diminished thy stated portion; and I gave thee up unto the will of those that hate thee, the daughters of the Philistines, who were made to blush for thy incestuous course.
28 Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
Then didst thou play the harlot with the sons of Asshur, because thou wast unsatiable: yea, thou didst play the harlot with them, and wast even then not satisfied.
29 Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
And thou didst multiply thy lewdness with the traders' land as far as Chaldea; and even with this wast thou not satisfied.
30 “‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
How very corrupt is thy heart, saith the Lord Eternal, seeing thou didst all these things, deeds of an abandoned lewd woman;
31 Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
Seeing that thou didst build thy eminences at the corner of every road, and make thy elevations in every street; and wast not like a harlot, as thou scornedst the wages.
32 “‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
O thou adulterous wife! who, while bound to her husband, receiveth strangers!
33 Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
Unto all harlots they give presents; but thou hast given thy presents to all thy lovers, and hast bribed them, that they might come unto thee from every side in thy acts of lewdness.
34 Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
And the reverse was the case with thee from [other] women in thy acts of lewdness, that men did not follow thee to seek thy lewd caresses; and because thou gavest the wages, and no wages were given thee: so was it the reverse with thee.
35 “‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
Therefore, O harlot, hear the word of the Lord!
36 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
Thus hath said the Lord Eternal, Whereas thy wealth was squandered, and thy nakedness was uncovered through thy lewd acts with thy lovers, and with all thy abominable idols, and for the blood of thy children, whom thou didst give unto them:
37 saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
Therefore, behold, I will gather all thy lovers, whom thou hast given pleasure, and all whom thou hast loved, together with all whom thou hast hated, —yea, I will gather them all round about thee, and will uncover thy nakedness unto them, that they may see all thy nakedness.
38 Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
And I will judge thee, as adulteresses and women that shed blood are judged; and I will bring upon thee the blood of fury and jealousy.
39 Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
And I will also give thee up into their hand, and they shall pull down thy eminences, and shall break down thy elevations; and they shall strip thee of thy clothes, and they shall take thy elegant ornaments, and leave thee naked and bare.
40 Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
And they shall bring up against thee an assembly, and they shall stone thee with stones, and thrust thee through with their swords;
41 Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
And they shall burn thy houses with fire, and execute punishments on thee before the eyes of many women: and I will cause thee to cease from being a harlot, and also the wages [of sin] shalt thou not give any more.
42 Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
And then will I assuage my fury on thee, and my jealousy shall depart from thee, and I will be quiet, and will be no more angry.
43 “‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
Because that thou didst not remember the days of thy youth, but didst irritate me with all these things: behold, therefore I also will bring thy course upon thy head, saith the Lord Eternal, and thou shalt no more commit incest with all thy [other] abominations.
44 “‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
Behold, every one that speaketh in proverbs shall use this proverb against thee, saying, As the mother is, so is her daughter.
45 Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
Thou art thy mother's daughter, loathing her husband and her children; and thou art the sister of thy sisters, who have loathed their husbands and their children: your mother was a Hittite, and your father an Emorite.
46 Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
And thy elder sister is Samaria, she with her daughters, that dwelleth at thy left hand, and thy younger sister, that dwelleth at thy right hand, is Sodom with her daughters.
47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
Yet not even in their ways didst thou walk, nor act according to their abominations: as though this were quite too little, and thou wast more corrupt than they in all thy ways.
48 Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
As I live, saith the Lord Eternal, Sodom thy sister, she with her daughters, hath not done as thou hast done, thou with thy daughters.
49 “‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
Behold, this was the iniquity of thy sister Sodom: Pride, abundance of food, and prosperous security were hers and her daughters'; but the hand of the poor and needy did she not strengthen.
50 Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
And they became haughty, and committed abominations before me: therefore did I remove them when I saw their course.
51 Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
And Samaria hath not committed even the half of thy sins; but thou didst multiply thy abominations more than they; and thou hast justified thy sisters through all thy abominations which thou hast done.
52 Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
Bear then thou also thy own confusion, which thou didst adjudge unto each of thy sisters; through thy sins, which thou hast committed more abominably than they, are they made more righteous than thou: therefore thou also—be ashamed, and bear thy confusion, since thou hast justified thy sisters.
53 “‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
And I will bring back again their captivity, the captivity of Sodom and her daughters, and the captivity of Samaria and her daughters, and the captivity of the captives in the midst of them:
54 domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
In order that thou mayest bear thy confusion, and mayest be confounded because of all that thou hast done, when thou art a comfort unto them.
55 ’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
And thy sisters, Sodom and her daughters, shall return to their former state, and Samaria and her daughters shall return to their former state, and thou and thy daughters shall return to your former state.
56 Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
And was not thy sister Sodom a report in thy mouth in the days of thy pride,
57 kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
Before yet thy wickedness was discovered, as at the time of the reproach of the daughters of Syria, and all those round about her, the daughters of the Philistines, who taunted thee on all sides?
58 Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
Thy incest and thy abominations, —thou thyself hadst to bear them, saith the Lord.
59 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
For thus hath said the Lord Eternal, I will even deal with thee as thou hast done, thou who hast despised the oath by breaking the covenant.
60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
Nevertheless will I indeed remember my covenant with thee in the days of thy youth, and I will establish unto thee an everlasting covenant.
61 Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
And thou shalt then remember thy ways, and be confounded, when thou receivest thy sisters, both those that are older than thou and younger than thou: and I will give them unto thee for daughters, though not because thou wast faithful to the covenant.
62 Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
And I will establish my covenant with thee; and thou shalt know that I am the Lord:
63 Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
In order that thou mayest remember, and feel ashamed, and never open thy mouth any more because of thy confusion, when I forgive thee for all that thou hast done, saith the Lord Eternal.