< Ezekiyel 16 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover the word of the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
Son of man, testify to Jerusalem [of] her iniquities;
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
and thou shalt say, Thus saith the Lord to Jerusalem; Thy root and thy birth are of the land of Chanaan: thy father was an Amorite, and thy mother a Chettite.
4 A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
And [as for] thy birth in the day wherein thou wast born, thou didst not bind thy breasts, and thou wast not washed in water, neither wast thou salted with salt, neither wast thou swathed in swaddling-bands.
5 Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
Nor did mine eye pity thee, to do for thee one of all these things, to feel at all for thee; but thou wast cast out on the face of the field, because of the deformity of thy person, in the day wherein thou wast born.
6 “‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
And I passed by to thee, and saw thee polluted in thy blood; and I said to thee, [Let there be] life out of thy blood:
7 Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
increase; I have made thee as the springing grass of the field. So thou didst increase and grow, and didst enter into great cities: thy breasts were set, and thy hair grew, whereas thou wast naked and bare.
8 “‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And I passed by thee and saw thee, and, behold, [it was] thy time and a time of resting; and I spread my wings over thee, and covered thy shame, and swear to thee: and I entered into covenant with thee, saith the Lord, and thou becamest mine.
9 “‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
And I washed thee in water, and washed thy blood from thee, and anointed thee with oil.
10 Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
And I clothed thee with embroidered [garments], and clothed thee beneath with purple, and girded thee with fine linen, and clothed thee with silk,
11 Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
and decked thee also with ornaments, and put bracelets on thine hands, and a necklace on thy neck.
12 na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
And I put a pendant on thy nostril, and rings in thine ears, and a crown of glory on thine head.
13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
So thou wast adorned with gold and silver; and thy raiment was of fine linen, and silk, and variegated work: thou didst eat fine flour, and oil, and honey, and didst become extremely beautiful.
14 Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And thy name went forth among the nations for thy beauty: because it was perfected with elegance, [and] in the comeliness which I put upon thee, saith the Lord.
15 “‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
Thou didst trust in thy beauty, and didst go a-whoring because of thy renown, and didst pour out thy fornication on every passer by.
16 Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
And thou didst take of thy garments, and madest to thyself idols of needlework, and didst go a-whoring after them; therefore thou shalt never come in, nor shall [the like] take place.
17 Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
And thou tookest thy fair ornaments of my gold and of my silver, of what I gave thee, and thou madest to thyself male images, and thou didst commit whoredom with them.
18 Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
And thou didst take thy variegated apparel and didst clothe them, and thou didst set before them mine oil and mine incense.
19 Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And [thou tookest] my bread which I gave thee, ([yea] I fed thee with fine flour and oil and honey) and didst set them before them for a sweet-smelling savour: yea, it was so, saith the Lord.
20 “‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
And thou tookest thy sons and thy daughters, whom thou borest, and didst sacrifice [these] to them to be destroyed. Thou didst go a-whoring as [if that were] little,
21 Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
and didst slay thy children, and gavest them up in offering them to them for an expiation.
22 Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
This is beyond all thy fornication, and thou didst not remember thine infancy, when thou wast naked and bare, [and] didst live [though] defiled in thy blood.
23 “‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
And it came to pass after all thy wickedness, saith the Lord,
24 kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
that thou didst build thyself a house of fornication, and didst make thyself a public place in every street;
25 A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
and on the head of every way thou didst set up thy fornications, and didst defile thy beauty, and didst open thy feet to every passer by, and didst multiply thy fornication.
26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
And thou didst go a-whoring after the children of Egypt thy neighbors, great of flesh; and didst go a-whoring, often to provoke me to anger.
27 Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
And if I stretch out my hand against thee, then will I abolish thy statutes, and deliver [thee] up to the wills of them that hate thee, [even to] the daughters of the Philistines that turned thee aside from the way wherein thou sinned.
28 Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
And thou didst go a-whoring to the daughters of Assur, and not even thus wast thou satisfied; yea, thou didst go a-whoring, and wast not satisfied.
29 Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
And thou didst multiply thy covenants with the land of the Chaldeans; and not even with these wast thou satisfied.
30 “‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
Why should I make a covenant with thy daughter, saith the Lord, while thou doest all these things, the works of a harlot? and thou hast gone a-whoring in a threefold degree with thy daughters.
31 Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
Thou hast built a house of harlotry in every top of a way, and hast set up thine high place in every street; and thou didst become as a harlot gathering hires.
32 “‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
An adulteress resembles thee, taking rewards of her husband.
33 Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
She has even given rewards to all that went a-whoring after her, and thou hast given rewards to all thy lovers, yea, thou didst load them with rewards, that they should come to thee from every side for thy fornication.
34 Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
And there has happened in thee perverseness in thy fornication beyond [other] women, and they have committed fornication with thee, in that thou givest hires over and above, and hires were not given to thee; and [thus] perverseness happened in thee.
35 “‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
Therefore, harlot, hear the word of the Lord:
36 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
Thus saith the Lord, Because thou hast poured forth thy money, therefore thy shame shall be discovered in thy harlotry with thy lovers, and [with] regard to all the imaginations of thine iniquities, and for the blood of thy children which thou hast given to them.
37 saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
Therefore, behold, I [will] gather all thy lovers with whom thou hast consorted, and all whom thou hast loved, with all whom thou didst hate; and I will gather them against thee round about, and will expose thy wickedness to them, and they shall see all thy shame.
38 Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
And I will be avenged on thee with the vengeance of an adulteress, and I will bring upon thee blood of fury and jealousy.
39 Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
And I will deliver thee into their hands, and they shall break down thy house of harlotry, and destroy thine high place; and they shall strip thee of thy garments, and shall take thy proud ornaments, and leave thee naked and bare.
40 Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
And they shall bring multitudes upon thee, and they shall stone thee with stones, and pierce thee with their swords.
41 Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
And they shall burn thine houses with fire, and shall execute vengeance on thee in the sight of many women: and I will turn thee back from harlotry, and I will no more give [thee] rewards.
42 Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
So will I slacken my fury against thee, and my jealousy shall be removed from thee, and I will rest, and be no more careful [for thee].
43 “‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
Because thou didst not remember thine infancy, and thou didst grieve me in all these things; therefore, behold, I have recompensed thy ways upon thine head, saith the Lord: for thus hast thou wrought ungodliness above all thine [other] iniquities.
44 “‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
These are all the things they have spoken against thee in a proverb, saying,
45 Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
As is the mother, so is thy mother's daughter: thou art she that has rejected her husband and her children; and the sisters of thy sisters have rejected their husbands and their children: your mother was a Chettite, and [your] father an Amorite.
46 Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
Your elder sister who dwells on thy left hand is Samaria, she and her daughters: and thy younger sister, that dwells on the right hand, is Sodom and her daughters.
47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
Yet notwithstanding thou hast not walked in their ways, neither hast thou done according to their iniquities within a little, but thou hast exceeded them in all thy ways.
48 Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
[As] I live, saith the Lord, this Sodom and her daughters have not done as thou and thy daughters have done.
49 “‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
Moreover this was the sin of thy sister Sodom, pride: she and her daughters lived in pleasure, in fullness of bread [and] in abundance: this belonged to her and her daughters, and they helped not the hand of the poor and needy.
50 Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
And they boasted, and wrought iniquities before me: so I cut them off as I saw [fit].
51 Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
Also Samaria has not sinned according to half of thy sins; but thou hast multiplied thine iniquities beyond them, and thou hast justified thy sisters in all thine iniquities which thou hast committed.
52 Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
Thou therefore bear thy punishment, for that thou hast corrupted thy sisters by thy sins which thou hast committed beyond them; and thou hast made them [appear] more righteous than thyself: thou therefore be ashamed, and bear thy dishonour, in that thou hast justified thy sisters.
53 “‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
And I will turn their captivity, [even] the captivity of Sodom and her daughters; and I will turn the captivity of Samaria and her daughters; and I will turn thy captivity in the midst of them:
54 domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
that thou mayest bear thy punishment, and be dishonoured for all that thou hast done in provoking me to anger.
55 ’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
And thy sister Sodom and her daughters shall be restored as they were at the beginning, and thou and thy daughters shall be restored as ye were at the beginning.
56 Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
And surely thy sister Sodom was not mentioned by thy mouth in the days of thy pride:
57 kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
before thy wickedness was discovered, even now thou art the reproach of the daughters of Syria, and of all that are round about her, [even] of the daughters of the Philistines that compass thee round about.
58 Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
[As for] thine ungodliness and thine iniquities, thou hast borne them, saith the Lord.
59 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
Thus saith the Lord; I will even do to thee as thou hast done, as thou hast dealt shamefully in these things to transgress my covenant.
60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
And I will remember my covenant [made] with thee in the days of thine infancy, and I will establish to thee an everlasting covenant.
61 Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
Then thou shalt remember thy way, and shalt be utterly dishonoured when thou receivest thine elder sisters with thy younger ones: and I will give them to thee for building up, but not by thy covenant.
62 Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
And I will establish my covenant with thee; and thou shalt know that I am the Lord:
63 Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
that thou mayest remember, and be ashamed, and mayest no more be able to open thy mouth for thy shame, when I am reconciled to thee for all that thou hast done, saith the Lord.

< Ezekiyel 16 >