< Ezekiyel 15 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
2 “Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
“İnsanoğlu, asma odununun herhangi bir orman ağacının dalından daha fazla değeri var mı?
3 An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
Asma odunundan yararlı bir şey yapılabilir mi? Ya da üzerine eşya asmak için ondan askı yaparlar mı?
4 Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
Yakıt olarak ateşe atılır da ateş odunun iki ucunu yakıp ortasını kömürleştirince, işe yarar mı?
5 In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
Yanmadan önce işe yaramadıysa, yanıp kömür haline geldikten sonra bir işe yarar mı?
6 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
“Bu nedenle Egemen RAB şöyle diyor: Orman ağaçları arasında asma odununu nasıl yakıt olarak ateşe verdimse, Yeruşalim'de yaşayan halka da aynısını yapacağım.
7 Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Onlara yüz çevireceğim. Şimdi ateşten kurtulsalar bile, ateş onları yine de yakıp yok edecek. Onlara yüz çevirince, benim RAB olduğumu anlayacaksınız.
8 Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Ülkeyi viraneye çevireceğim. Çünkü bana sadakatsizlik ettiler. Egemen RAB böyle diyor.”