< Ezekiyel 15 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
Fils d'homme, que vaut le bois de la vigne plus que les autres bois? et les sarments plus que les branches des arbres d'une forêt?
3 An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
En prendra-t-on du bois pour en faire quelque ouvrage? ou en prendra-t-on un croc pour y pendre quelque chose?
4 Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
Voici, on le met au feu pour être consumé: le feu a consumé aussitôt ses deux bouts, et le milieu est en feu; vaut-il rien pour quelque ouvrage?
5 In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
Voici, quand il est entier, on n'en fait aucun ouvrage; combien moins quand le feu l'aura consumé, et qu'il sera brûlé, sera-t-il propre pour quelque ouvrage?
6 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: comme le bois de la vigne est tel entre les arbres d'une forêt, que je l'ai assigné au feu pour être consumé; ainsi je livrerai les habitants de Jérusalem.
7 Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Et je me tournerai contre eux; seront-ils sortis du feu? encore le feu les consumera; et vous saurez que je suis l'Eternel, quand je me serai tourné contre eux.
8 Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et je ferai que le pays ne sera que désolation; parce qu'ils ont commis une infidélité, dit le Seigneur l'Eternel.

< Ezekiyel 15 >