< Ezekiyel 15 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of Yahweh came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
“Son of man, how is a vine better than any tree with branches that is among the trees in a forest?
3 An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
Do people take wood from a vine to make anything? Or do they make a peg from it to hang anything on it?
4 Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
See! If it is thrown into a fire as fuel, and if the fire has burned both of its ends and also the middle, is it good for anything?
5 In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
See! When it was complete, it could not make anything; surely then, when the fire has burned, then it still will not make anything useful.
6 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
Therefore the Lord Yahweh says this: Unlike the trees in the forests, I have given the vine as fuel for fires; I will act in the same way toward the inhabitants of Jerusalem.
7 Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
For I will set my face against them. Though they come out from the fire, yet the fire will consume them; so you will know that I am Yahweh, when I set my face against them.
8 Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Then I will make the land into an abandoned wasteland because they have committed sin—this is the Lord Yahweh's declaration.”