< Ezekiyel 15 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Yahweh came unto me saying:
2 “Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
Son of man, What can the vine-tree be more than any other tree, —any branch which hath been found among the trees of the forest?
3 An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
Shall there be taken from it wood, to be made into any work? Or will men take therefrom a peg, to hang thereon any vessel?
4 Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
Lo! into the fire, it is given up for fuel, — The two ends thereof, doth the fire devour, And the middle thereof is charred, Is it fit for any work?
5 In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
Lo! while it was yet whole, it could not be made into any work, — how much less when! the fire hath devoured it. and it is charred, can it still be made into any work?
6 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
Therefore, Thus, saith My Lord Yahweh, As a vine-tree among the trees of the forest, which I have given up to the fire for fuel, so have I given up the inhabitants of Jerusalem.
7 Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Therefore will I set my face against them, Out of one fire, have they come forth But another fire, shall devour them, —So shall ye know that, I, am Yahweh, by my setting my face against them;
8 Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
I will therefore give up the land as a desolation, —because they have committed treachery, Declareth My Lord., Yahweh.

< Ezekiyel 15 >