< Ezekiyel 15 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
“Son of man, is wood from a vine better than the wood from any other tree in the forest?
3 An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
Can you make anything useful from vine wood? Can you use it to make even just a peg to hang up pots and pans?
4 Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
No, you just throw it on the fire to keep the fire burning. Even then the fire burns both ends, but only chars the middle part. Can you use it for anything?
5 In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
Even before you burned it you couldn't make it into anything useful. It's even less useful once the fire has burned and charred it!
6 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
So this is what the Lord God says: In the same way that I have taken the wood of a vine from the forest and thrown it on the fire to be burned, so I'm going to throw away the people of Jerusalem.
7 Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
I will turn against them. While they might have escaped this fire, another fire is going to burn them up. When I turn against them, then you will know that I am the Lord.
8 Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
I'm going to turn the country into a wasteland, because they were unfaithful to me, declares the Lord God.”

< Ezekiyel 15 >