< Ezekiyel 14 >
1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
İsrail ileri gelenlerinden kimisi gelip yanıma oturdu.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
O sırada RAB bana şöyle seslendi:
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
“İnsanoğlu, bu adamların yüreği putlara bağlı. Diktikleri putların kendilerini günaha sokmasına olanak veriyorlar. Öyleyse onların bana danışmasına izin vermeli miyim?
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
Bunun için onlarla konuş ve de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Yüreğini puta bağlayan, diktiği putun kendisini günaha sokmasına olanak veren, sonra da peygambere danışmaya gelen her İsrailli'ye putlarının çokluğuna göre ben RAB kendim karşılık vereceğim.
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
Bunu, putları yüzünden bana sırt çeviren İsrail halkının yüreğini yeniden kendime çekmek için yapacağım.’
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
“Bu yüzden İsrail halkına de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Geri dönün! Putlarınızdan vazgeçin, iğrenç uygulamalarınızı bırakın!
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
“‘İsrail halkından biri ya da İsrail'de yaşayan bir yabancı benden ayrılır, yüreğini putlara bağlar, diktiği putların kendisini günaha sokmasına olanak verir, sonra da bana danışmak üzere bir peygambere giderse, ben RAB kendim ona karşılık vereceğim.
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
O kişiye karşı çıkacağım. Onu bir belirti, bir alay konusu yapıp halkımın arasından atacağım. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
“‘Bir peygamber ayartılır da bir söz söylerse, onu ayartan benim. Elimi ona karşı uzatacağım, onu halkım İsrail'in arasından çıkarıp yok edeceğim.
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
Suçlarının cezasını çekecekler. Peygamber de ona danışan da aynı şekilde cezalandırılacak.
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Böylece İsrail halkı bir daha benden ayrılmayacak, günahlarıyla kendilerini kirletmeyecekler. Onlar halkım olacaklar, ben de onların Tanrısı olacağım. Egemen RAB böyle diyor.’”
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
“İnsanoğlu, eğer bir ülke bana sadakatsizlik eder, günah işlerse, ben de o ülkeye karşı elimi uzatır, onu her türlü yiyecekten yoksun bırakır, üzerine kıtlık gönderir, insanları ve hayvanları yok edersem;
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
şu üç adam –Nuh, Daniel, Eyüp– orada olsalar bile, doğruluklarıyla ancak kendi canlarını kurtarabilirler. Egemen RAB böyle diyor.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
“Ya da ülkeye yabanıl hayvanlar gönderirsem ve ülkeyi kimsesiz bırakırlarsa, ülke viraneye döner, hayvanlar yüzünden kimse içinden geçemezse;
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
Varlığım hakkı için diyor Egemen RAB, bu üç kişi o ülkede yaşasa bile, ne oğullarını ne de kızlarını kurtarabilirler. Ancak kendi canlarını kurtarabilirler. Ülke ise viraneye döner.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
“Ya da o ülkeye kılıç gönderir, ‘Kılıç ülkeyi yarsın’ der, oradaki insanları ve hayvanları yok edersem;
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
varlığım hakkı için diyor Egemen RAB, bu üç kişi orada olsa bile, ne oğullarını ne de kızlarını kurtarabilirler. Ancak kendi canlarını kurtarabilirler.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
“O ülkeye salgın hastalık gönderir, kan dökerek öfkemi yağdırır, oradaki insanları ve hayvanları yok edersem;
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
varlığım hakkı için diyor Egemen RAB, Nuh, Daniel ve Eyüp orada olsa bile, ne oğullarını ne de kızlarını kurtarabilirler. Doğruluklarıyla ancak kendi canlarını kurtarabilirler.
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
“Egemen RAB şöyle diyor: Yeruşalim'deki insanları ve hayvanları yok etmek için üzerine dört ağır yargımı –kılıcı, kıtlığı, yabanıl hayvanları, salgın hastalığı– gönderdiğimde daha neler neler olacak!
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
Orada sağ bırakılacak kimi oğullarınız, kızlarınız olacak, çıkıp yanınıza gelecekler. Onların davranışlarını ve yaptıklarını görünce, Yeruşalim'in başına getirdiğim yıkımdan ve her tür felaketten avuntu bulacaksınız.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Onların davranışlarını ve yaptıklarını görünce avutulacak, Yeruşalim'in başına getirdiklerimin amaçsız olmadığını anlayacaksınız. Egemen RAB böyle diyor.”