< Ezekiyel 14 >
1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
A LAILA hele mai kekahi mau luna kahiko o ka Iseraela, a noho iho imua o'u.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Hiki mai la hoi ka olelo a Iehova ia'u i mai la,
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
E ke keiki a ke kanaka, ua kukulu keia poe kanaka i ko lakou mau kii iloko o ko lakou mau naau, a waiho iho i ko lakou mea hoowalewale i ka hewa imua o ko lakou alo; e ninauia mai anei au e lakou?
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
Nolaila, e olelo aku oe ia lakou, a e i aku ia lakou, Ke i mai nei Iehova ka Haku penei; O kela kanaka keia kanaka o ka ohana a Iseraela i kukulu i kona mau kii iloko o kona naau, a i waiho iho i kona mea hoowalewale i ka hewa imua o kona alo, a hele mai hoi i ke kaula; na'u na Iehova e hai aku i ka mea i hele mai e like me ka nui o kona poe kii;
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
I hopu au i ka ohana a Iseraela iloko o ko lakou naau iho, no ka mea, ua aea lakou mai o'u aku nei ma ko lakou mau kii.
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
Nolaila e olelo aku oe i ka ohana a Iseraela, Ke i mai nei Iehova ka Haku penei; E mihi oukou, a e huli mai, mai ko oukou mau kii mai, a e hoohuli i ko oukou mau maka mai ko oukou mau mea e inainaia a pau.
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
No ka mea, o kela mea keia mea o ka ohana a Iseraela, a o ka malihini e noho iki ana iloko o ka Iseraela, i hookaawale ia ia iho mai o'u aku nei, a kukulu hoi i kona mau kii iloko o kona naau, a waiho iho hoi i kona mea e hoowalewale ai i ka hewa imua o kona alo. a hele mai hoi i ke kaula e ninau mai no'u; na'u na Iehova e hai aku ia ia ma o'u iho no.
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
A e hooku e au i ko'u wahi maka i kela kanaka, a e hoolilo au ia ia i hoailona, a i hua olelo hoohiki; a e oki aku au ia ia mai waena aku o ko'u poe kanaka; a e ike no hoi oukou owau no Iehova.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
A ina e puni ke kaula i kana olelo ana i kekahi mea, ua puni ia kaula ia'u ia Iehova. A e kikoo aku au i ko'u lima maluna ona, a e luku aku au ia ia mai waenakonu aku o ko'u poe kanaka ka Iseraela.
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
A e halihali lakou i ka hoopaiia o ko lakou hewa. E like ka hoopai ana i ke kaula me ka hoopai ana i ka mea i imi aku;
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
I ole e auwana hou aku ka ohana a Iseraela mai o'u aku nei, i ole hoi e haumia hou me ko lakou lawehala ana, aka, e lilo lakou i poe kanaka no'u, a owau no hoi i Akua no, lakou, wahi a Iehova ka Haku.
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Hiki hou mai la ka olelo a Iehova ia'u, i mai la,
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
E ke keiki a ke kanaka, i ka wa e hana hewa loa mai ai ka aina ia'u, e kikoo aku au i ko'u lima maluna iho ona, a e uhai au i ke kookoo o kana berena, a e hoouna aku au i ka wi maluna ona, a e oki aku i na kanaka me na holoholona mai ona aku la;
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Ina o keia mau kanaka ekolu ka iloko ona, o Noa, Dauiela a me Ioba, o ko lakou mau uhane iho ka lakou e hoopakele ai ma ko lakou pono, wahi a Iehova ka Haku.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
Ina e hoohele ae au i na holoholona ino iwaena o ka aina, a oki loa ia lakou, a neoneo loa i ole ai e hele ae ke kanaka mawaena no ua poe holoholona la;
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
Ina o keia mau kanaka ekolu ka iloko ona, ma ko'u ola ana, wahi a Iehova ka Haku, aole lakou e hoopakele i na keikikane me na kaikamahine, o lakou wale no ke hoopakeleia, aka, e neoneo no ka aina.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
A ina lawe au i ka pahikaua maluna o ka aina, a e olelo aku, E ka pahikaua, e hele oe mawaeua o ka aina; a oki aku au i na kanaka a me na holoholona mai ona aku la;
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
Ina o keia mau kanaka ekolu ka iloko ona, ma ko'u ola ana, wahi a Iehova ka Haku, aole lakou e hoopakele i na keikikane, aole hoi i na kaikamahine; o lakou wale no ke hoopakeleia.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
A ina e hoouna au i ka mai ahulau i kela aina, a e ninini aku i ko'u huhu maluna ona me ke koko, e oki aku i kanaka pu me ka holoholona,
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
Ina o Noa, Daniela a me Ioba ka iloko ona, ma ko'u ola ana, wahi a Iehova ka Haku, aole lakou e hoopakele i ke keikikane, aole hoi i ke kaikamahine; o ko lakou mau uhane iho ka lakou e hoopakele ai ma ko lakou pono.
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
No ka mea, ke i mai nei Iehova ka Haku, penei; E kela aku keia i ka wa e hoouna aku ai au i kuu mau mea hoopai kaumaha a eha maluna o Ierusalema, i ka pahikaua, a me ka wi, a me ka holoholona ino, a me ka mai auhulau, e oki aku mai laila aku i kanaka pu me ka holoholona.
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
Aka, eia hoi, e koe no ke koena iloko ona e laweia'e iwaho, o na keikikane a me na kaikamahine; aia hoi, e puka mai lakou io oukou la, a e ike oukou i ko lakou aoao a me ka lakou hana ana; a e hooluoluia oukou no ka ino a'u i hooili ae ai maluna o Ierusalema, no na mea a pau a'u i kau ai maluna ona.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
A e hooluolu lakou ia oukou, aia ike oukou i ko lakou mau aoao a me ka lakou hana ana; a e ike oukou aole au i hana kumu ole i na mea a pau a'u i hana'i iloko ona, wahi a Iehova ka Haku.