< Ezekiyel 14 >

1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
Or quelques-uns des Anciens d'Israël vinrent vers moi, et s'assirent devant moi.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
Fils d'homme, ces gens-ci ont posé leurs idoles dans leurs cœurs, et ont mis devant leur face l'achoppement de leur iniquité; serais-je recherché d'eux sérieusement?
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
C'est pourquoi parle-leur, et leur dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel. Quiconque de la maison d'Israël aura posé ses idoles dans son cœur, et aura mis devant sa face l'achoppement de son iniquité, et viendra vers le Prophète, Je [suis] l'Eternel, je lui ai répondu [tout] ce que je lui veux répondre, [puisqu'il] vient avec la multitude de ses idoles.
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
Afin que je prenne la maison d'Israël par leur propre cœur, car eux tous se sont éloignés de moi par leurs idoles.
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
C'est pourquoi dis à la maison d'Israël: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel, convertissez-vous, et faites qu'on se retire de vos idoles, et détournez-vous de toutes vos abominations.
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
Car quiconque de la maison d'Israël, ou des étrangers qui séjournent en Israël, se sera séparé de moi, et aura posé ses idoles dans son cœur, et mis l'achoppement de son iniquité devant sa face, s'il vient vers le Prophète pour m'interroger par lui, je suis l'Eternel, on lui a répondu tout ce qu'on a à lui répondre de ma part.
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Et je me tournerai contre cet homme, et je le ferai servir de signe, et de jouet, et je le retrancherai du milieu de mon peuple; et vous saurez que je [suis] l'Eternel.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
Et s'il arrive que le Prophète soit séduit, et qu'il profère quelque parole, moi l'Eternel j'aurai séduit ce Prophète-là, et j'étendrai ma main sur lui, et je l'exterminerai du milieu de mon peuple d'Israël;
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
Et ils porteront la peine de leur iniquité; la peine de l'iniquité du Prophète sera toute telle que la peine de celui qui l'aura interrogé;
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Afin que la maison d'Israël ne s'éloigne plus de moi, et qu'ils ne se souillent plus par tous leurs crimes; alors ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu, dit le Seigneur l'Eternel.
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
Fils d'homme, lorsqu'un pays aura péché contre moi, en commettant une infidélité, et que j'aurai étendu ma main contre lui, et que je lui aurai rompu le bâton du pain, et envoyé la famine, et retranché du milieu de lui tant les hommes que les bêtes;
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et que ces trois hommes, Noé, Daniel et Job, y seraient, ils délivreraient leurs âmes par leur justice, dit le Seigneur l'Eternel.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
Si je fais passer les mauvaises bêtes par ce pays-là, et qu'elles le désolent, tellement que ce [ne] soit [que] désolation, sans qu'il y ait personne qui [y] passe à cause des bêtes;
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
[Et] que ces trois hommes-là s'y trouvent; je suis vivant, dit le Seigneur l'Eternel, qu'ils ne délivreront ni fils ni filles, eux seulement seront délivrés, et le pays [ne] sera [que] désolation.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
Ou si je fais venir l'épée sur ce pays-là, et si je dis: que l'épée passe par le pays, et qu'elle en retranche les hommes et les bêtes;
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
Si ces trois hommes-là se trouvent au milieu du pays, je suis vivant, dit le Seigneur l'Eternel, qu'ils ne délivreront ni fils, ni filles; mais eux seulement seront délivrés.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
Ou [si] j'envoie la mortalité sur ce pays-là, et que je répande ma colère contre lui, jusques à faire ruisseler le sang, tellement que je retranche du milieu de lui les hommes et les bêtes;
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
Et que Noé, Daniel et Job s'y trouvent, je [suis] vivant, dit le Seigneur l'Eternel, qu'ils ne délivreront ni fils ni filles; [mais] ils délivreront leurs âmes par leur justice.
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
Car ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: combien plus quand j'aurai envoyé mes quatre plaies mortelles, l'épée, et la famine, et les bêtes nuisibles, et la mortalité, contre Jérusalem, pour en retrancher les hommes et les bêtes?
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
Et toutefois, voici, quelques réchappés y demeureront de reste, [savoir] ceux qu'on s'en va faire sortir, et fils et filles; voici, ils viennent vers vous, et vous verrez leur train [de vie], et leurs actions, et vous serez satisfaits du mal que j'aurai fait venir contre Jérusalem, et de tout ce que j'aurai fait venir sur elle.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Vous en serez, dis-je, satisfaits, lorsque vous aurez vu leur train [de vie], et leurs actions; et vous connaîtrez que je n'aurai point exécuté sans cause tout ce que j'aurai fait en elle, dit le Seigneur l'Eternel.

< Ezekiyel 14 >