< Ezekiyel 14 >
1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
Now certain men of the elders of Israel came to me, and sat before me.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying:
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
Son of man, these men have set up their idols in their heart, and have put the stumbling-block of their iniquity before their face; shall I hear them when they inquire of me?
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
Therefore speak with them, and say to them, Thus saith the Lord Jehovah: Every man of the house of Israel that setteth up his idols in his heart, and putteth the stumbling-block of his iniquity before his face, and cometh to the prophet, —I, Jehovah, will answer him according to the multitude of his idols;
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
that I may lay hold of the house of Israel in their hearts, because they are all estranged from me through their idols.
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
Therefore say to the house of Israel, Thus saith the Lord Jehovah: Turn ye, even turn yourselves from your idols, and from all your abominations turn ye your faces!
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
For every one of the house of Israel, or of the strangers that sojourn in Israel, who separateth himself from me, and setteth up his idols in his heart, and putteth the stumbling-block of his iniquity before his face, and cometh to the prophet to inquire of me through him, —I, Jehovah, will answer him by myself.
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
And I will set my face against that man, and will make him a sign and a proverb, and will cut him off from the midst of my people; and ye shall know that I am Jehovah.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
And when the prophet is deceived when he speaketh anything, I, Jehovah, have deceived that prophet; and I will stretch out my hand upon him, and will destroy him from the midst of my people Israel.
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
And they shall bear the punishment of their iniquity; the punishment of the prophet shall be even as the punishment of him that inquireth of him;
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
that the house of Israel may no more go astray from me, nor be polluted any more with all their transgressions; but that they may be my people, and I may be their God, saith the Lord Jehovah.
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Again the word of Jehovah came to me, saying:
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
Son of man, when a land sinneth against me, and grievously transgresseth, and I stretch out my hand against it, and break the staff of its bread, and send famine upon it, and cut off from it man and beast,
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
though these three men were in it, Noah, Daniel, and Job, they should deliver only themselves by their righteousness, saith the Lord Jehovah.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
When I cause wild beasts to pass through the land, and they spoil it, and it be desolate so that none passeth through it because of the beasts,
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
though these three men were in it, as I live, saith the Lord Jehovah, they should deliver neither sons nor daughters; they only should be delivered, but the land should be desolate.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
Or when I bring a sword upon that land, and say, Sword, go through the land so that I cut off from it man and beast,
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
though these three men were in it, as I live, saith the Lord Jehovah, they should deliver neither sons nor daughters, but they only should be delivered themselves.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
Or when I send a pestilence upon that land, and pour out my fury upon it in blood, to cut off from it man and beast,
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
though Noah, Daniel, and Job were in it, as I live, saith the Lord Jehovah, they should deliver neither son nor daughter; they should deliver only themselves by their righteousness.
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
Therefore thus saith the Lord Jehovah: How much more, when I send my four grievous judgments against Jerusalem, the sword, and the famine, and the wild beast, and the pestilence, to cut off from it man and beast?
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
Yet behold, therein shall be left a remnant that shall be brought forth, sons and daughters. Behold, they shall come forth to you, and ye shall see their way and their doings, and ye shall be comforted concerning the evil which I have brought upon Jerusalem, even concerning all which I have brought upon her.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
They shall comfort you, when ye see their ways and their doings; and ye shall know that not without cause I have done all that I have done to her, saith the Lord Jehovah.