< Ezekiyel 14 >

1 Waɗansu dattawan Isra’ila suka zo wurina suka zauna a ƙasa a gabana.
And men from [the] elderly of Israel come to me, and sit before me.
2 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, saying,
3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun kafa gumaka a cikin zukatansu suka sa mugayen abubuwan sa tuntuɓe a gabansu. Zan bar su, su taɓa nemi ni?
“Son of man, these men have caused their idols to go up on their heart, and they have put the stumbling-block of their iniquity before their faces; am I inquired of at all by them?
4 Saboda haka ka yi musu magana ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da wani mutumin Isra’ila ya kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuma sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina game da babban bautar gumakarsa.
Therefore, speak with them, and you have said to them, Thus said Lord YHWH: Everyone of the house of Israel who causes his idols to go up to his heart, and sets the stumbling-block of his iniquity before his face, and has gone to the prophet—I, YHWH, have given an answer to him for this, for the abundance of his idols,
5 Zan yi haka don in sāke ƙame zukatan mutanen Isra’ila, waɗanda duk suka yashe ni don gumakansu.’
in order to catch the house of Israel by their heart, in that they have become estranged from off Me by their idols—all of them.
6 “Saboda haka ka faɗa wa gidan Isra’ila cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tuba! Ku juyo daga gumakanku ku kuma furta dukan ayyukanku masu banƙyama!
Therefore say to the house of Israel, Thus said Lord YHWH: Turn back, indeed, turn back from your idols, and turn back your faces from all your abominations,
7 “‘Duk sa’ad da mutumin Isra’ila ko baƙo mai zama a Isra’ila ya rabu da ni ya kuma kafa gumaka a cikin zuciyarsa ya kuna sa mugun abin tuntuɓe a gabansa sa’an nan ya tafi wurin annabi don yă neme ni, Ni Ubangiji zan amsa masa da kaina.
for everyone of the house of Israel, and of the sojourners who sojourn in Israel, who is separated from after Me, and causes his idols to go up to his heart, and sets the stumbling-block of his iniquity before his face, and has come to the prophet to inquire of him concerning Me, I, YHWH, have answered him for Myself;
8 Zan yi gāba da mutumin in kuma sa ya zama misali da kuma abin karin magana. Zan ware shi daga mutanena. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
and I have set My face against that man, and made him for a sign, and for allegories, and I have cut him off from the midst of My people, and you have known that I [am] YHWH.
9 “‘In kuma aka ruɗi annabin har ya yi annabci, Ni Ubangiji na rinjayi wannan annabi, zan kuma miƙa hannuna gāba da shi in hallaka shi daga cikin mutanena Isra’ila.
And the prophet, when he is enticed, and has spoken a word—I, YHWH, have enticed that prophet, and have stretched out My hand against him, and have destroyed him from the midst of My people Israel.
10 Za su ɗauki hakkin laifinsu annabin zai zama mai laifi daidai da wanda ya zo neman shawararsa.
And they have borne their iniquity: as the iniquity of the inquirer, so is the iniquity of the prophet;
11 Sa’an nan mutanen Isra’ila ba za su ƙara kauce daga gare ni ba, ba kuwa za su ƙara ƙazantar da kansu da dukan zunubansu ba. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
so that the house of Israel does not wander from after Me anymore, nor are they defiled with all their transgressions anymore, and they have been to Me for a people, and I am to them for God—a declaration of Lord YHWH.”
12 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, saying,
13 “Ɗan mutum, in wata ƙasa ta yi mini zunubi ta wurin rashin aminci na kuma miƙa hannuna gāba da ita don in toshe hanyar samun abincinta na kuma aika da yunwa a kanta na kashe mutanenta da dabbobinta,
“Son of man, when the land sins against Me to commit a trespass, and I have stretched out My hand against it, and broken the staff of bread for it, and sent famine into it, and cut off man and beast from it—
14 ko da waɗannan mutum uku Nuhu, Daniyel da kuma Ayuba suna a cikinta, za su iya ceton kansu ne kawai ta wurin adalcinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
and [despite] these three men [that] have been in its midst: Noah, Daniel, and Job—they [only] deliver their own soul by their righteousness,” a declaration of Lord YHWH.
15 “Ko kuwa in na aika da namun jeji su ratsa cikin wannan ƙasa suka kuma bar ta babu yaro, ta kuma zama kufai har babu wanda zai ratsa cikinta saboda namun jeji,
“If I cause an evil beast to pass through the land, and it has bereaved, and it has been a desolation, without any passing through because of the beast—
16 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da ma waɗannan mutum uku suna a cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto, amma ƙasar za tă zama kufai.
[despite] these three men in its midst—[as] I live,” a declaration of Lord YHWH, “they deliver neither sons nor daughters; they alone are delivered, and the land is a desolation.
17 “Ko kuma in na kawo takobi a kan wannan ƙasa na kuma ce, ‘Bari takobin ya ratsa cikin dukan ƙasar,’ na kuma kashe mutanenta da dabbobinsu,
Or [if] I bring a sword in against that land, and I have said: Sword, pass over through the land, and I have cut off man and beast from it—
18 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da waɗannan mutum uku suna cikinta, ba za su iya ceton’ya’yansu maza ko mata ba. Su kaɗai za a iya ceto.
and [despite] these three men in its midst—[as] I live,” a declaration of Lord YHWH, “they do not deliver sons and daughters, for they alone are delivered.
19 “Ko kuma in na aika da annoba a cikin wannan ƙasa na kuma yi fushi a kanta ta wurin kisa, ina kisan mutanenta da dabbobinsu,
Or [if] I send pestilence to that land, and I have poured out My fury against it in blood, to cut off man and beast from it—
20 muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ko da Nuhu, Daniyel da Ayuba suna a cikinta, ba za su iya ceton ɗansu ko’yarsu ba. Za su iya ceton kansu ne kaɗai ta wurin adalcinsu.
and [despite] Noah, Daniel, and Job, in its midst—[as] I live,” a declaration of Lord YHWH, “they deliver neither son nor daughter; they, by their righteousness, [only] deliver their own soul.”
21 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa balle fa sa’ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi takobi da yunwa da namun jeji da annoba don su kashe mutanenta da dabbobinsu!
For thus said Lord YHWH: “Although My four severe judgments—sword, and famine, and wild beast, and pestilence—I have sent to Jerusalem, to cut off man and beast from it,
22 Duk da haka za a sami mutanen da za su ragu’ya’ya maza da matan da za a fitar daga cikinta. Za su zo wurinka, kuma sa’ad da ka gan halinsu da ayyukansu, za ka ta’azantu game da bala’in da na kawo a kan Urushalima kowane bala’in da na kawo a kanta.
yet, behold, there has been left an escape in it, who are brought forth, sons and daughters, behold, they are coming forth to you, and you have seen their way, and their doings, and have been comforted concerning the calamity that I have brought in against Jerusalem, all that which I have brought in against it.
23 Za ka ta’azantu sa’ad da ka ga halinsu da kuma ayyukansu, gama za ka san cewa ban aikata wani abu a cikinta ba dalili ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And they have comforted you, for you see their way and their doings, and you have known that I have not done all that which I have done in her for nothing,” a declaration of Lord YHWH.

< Ezekiyel 14 >