< Ezekiyel 13 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In k meni je prišla Gospodova beseda, rekoč:
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
»Človeški sin, prerokuj zoper Izraelove preroke, ki prerokujejo in reci tem, ki prerokujejo iz svojih lastnih src: ›Poslušajte Gospodovo besedo:
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
›Tako govori Gospod Bog: ›Gorje nespametnim prerokom, ki sledijo svojemu lastnemu duhu in ničesar niso videli!‹
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Oh Izrael, tvoji preroki so podobni lisicam v puščavah.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Vi niste odšli gor v razpoke niti niste postavili ograje za Izraelovo hišo, da obstane v bitki na Gospodov dan.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Videli so ničnost in lažniva vedeževanja, rekoč: › Gospod govori, ‹ pa jih Gospod ni poslal. In druge so pripravili, da upajo, da bi potrdili besedo.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Mar niste videli praznega videnja in ali niste govorili lažnivega vedeževanja, medtem ko govorite: › To govori Gospod; ‹ čeprav nisem govoril?‹
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Zato tako govori Gospod Bog: ›Ker ste govorili prazne reči in videli laži, zato, glejte, jaz sem zoper vas, ‹ govori Gospod Bog.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
›In moja roka bo na prerokih, ki vidijo prazne reči in ki vedežujejo laži. Ne bodo v zboru mojega ljudstva niti ne bodo zapisani v zapisu Izraelove hiše niti ne bodo vstopili v Izraelovo deželo, in spoznali boste, da jaz sem Gospod Bog.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
Zato, celo zato so zapeljali moje ljudstvo, rekoč: ›Mir; ‹ pa tam ni bilo miru; in nekdo je zgradil zid in glej, drugi so ga ometali z neutrjeno malto.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Recite tistim, ki ga ometujejo z neutrjeno malto, da bo ta padel. Preplavljajoč naliv bo; oh, velika zrna toče bodo padala; in viharni veter ga bo razklal.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
Glejte, ko pade zid, ali vam ne bo rečeno: ›Kje je zmazek, s katerim ste ga namazali?‹
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Zato tako govori Gospod Bog: ›V svoji razjarjenosti ga bom celo razklal z viharnim vetrom; in tam bo preplavljajoč naliv v moji jezi in velika zrna toče v moji razjarjenosti, da ga použijejo.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Tako bom porušil zid, ki ste ga ometali z neutrjeno malto in ga porušim do tal, tako da bodo odkriti njegovi temelji in ta bo padel, vi pa boste použiti v njegovi sredi in spoznali boste, da jaz sem Gospod.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
Tako bom dovršil svoj bes nad zidom in nad temi, ki so ga ometali z neutrjeno malto in vam bom rekel: ›Zidu ni več niti tistih, ki so ga ometali;
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
namreč Izraelovih prerokov, ki prerokujejo glede [prestolnice] Jeruzalem in ki zanjo vidijo videnja miru, pa tam ni miru, ‹ govori Gospod Bog.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
›Prav tako ti, človeški sin, naravnaj svoj obraz zoper hčere svojega ljudstva, ki prerokujejo iz svojih lastnih src; in prerokuj zoper njih
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
ter reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Gorje ženskam, ki šivajo blazine k vsem odprtinam za rokave in izdelujejo naglavne rute na glavi vsake postave, da bi lovile duše! Hočete loviti duše mojega ljudstva in ali boste duše, ki prihajajo k vam, rešile žive?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
In ali me hočete oskruniti med mojim ljudstvom za prgišča ječmena in za koščke kruha, da ubijate duše, ki naj ne bi umrle in da rešujete duše žive, ki naj ne bi živele, z vašim laganjem mojemu ljudstvu, ki posluša vaše laži?‹
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
Zato tako govori Gospod Bog: ›Glejte, jaz sem zoper vaše blazine, s katerimi ste tam lovile duše, da jih pripravite leteti in iztrgal jih bom iz vaših rok in jaz bom pustil dušam oditi, celó dušam, ki jih vi lovite, da jih pripravite leteti.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
Tudi vse naglavne rute bom raztrgal in osvobodil svoje ljudstvo iz vaše roke in nič več ne bodo v vaši roki, da bi jih lovile; in spoznale boste, da jaz sem Gospod.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Ker ste z lažmi užalostile srce pravičnega, ki ga nisem užalostil; in okrepile roke zlobnega, da se ta ne bi vrnil iz svoje zlobne poti, [s tem] da ste mu obljubljale življenje,
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
zato ne boste več videle praznih reči niti božanskih vedeževanj, kajti jaz bom osvobodil svoje ljudstvo iz vaše roke, in spoznale boste, da jaz sem Gospod.«

< Ezekiyel 13 >