< Ezekiyel 13 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Опет ми дође реч Господња говорећи:
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
Сине човечји, пророкуј против пророка Израиљевих који пророкују, и реци тим који пророкују из свог срца: Чујте реч Господњу.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
Овако говори Господ Господ: Тешко лудим пророцима који иду за својим духом, а ништа нису видели.
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Пророци су твоји, Израиљу, као лисице по пустињама.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Не излазите на проломе и не ограђујете дом Израиљев да би се одржао у боју у дан Господњи.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Виде таштину и гатање лажно, па говоре: Господ каже, а Господ их није послао, и дају наду да ће се реч испунити.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Не виђате ли ташту утвару и не говорите ли лажно гатање? А опет кажете: Господ рече; а ја не рекох.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Зато овако вели Господ Господ: Зато што говорите таштину и видите лаж, за то ево мене на вас, говори Господ Господ.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
И рука ће моја бити против пророка који виде таштину и гатају лаж; неће их бити у збору народа мог, и у препису дома Израиљевог неће бити записани, нити ће доћи у земљу Израиљеву; и познаћете да сам ја Господ Господ.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
Зато, зато што преластише народ мој говорећи: Мир је, а мира не беше; и један озида зид, а други га намазаше кречем неваљалим;
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Реци оним што мажу неваљалим кречем да ће пасти; доћи ће силан дажд, и ви, камење великог града, пашћете и олуја ће развалити.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
И гле, кад падне зид, неће ли вам се рећи: Где је креч којим мазасте?
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Зато овако вели Господ Господ: Развалићу олујом у гневу свом, и силан ће дажд доћи у гневу мом, и камење великог града у јарости мојој да потре.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
И развалићу зид који намазасте неваљалим кречем, и оборићу га на земљу да ће му се открити темељ, и пашће, и ви ћете изгинути усред њега, и познаћете да сам ја Господ.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
И тако ћу навршити гнев свој на зиду и на онима који га мажу кречем неваљалим, и рећи ћу вам: Нема зида, нити оних који га мазаше,
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
Пророка Израиљевих који пророкују Јерусалиму и виде му утваре за мир, а мира нема, говори Господ Господ.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
А ти, сине човечји, окрени лице своје према кћерима народа свог, које пророкују из свог срца, и пророкуј против њих.
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
И реци: Овако вели Господ Господ: тешко онима које шију узглавља под све лактове и граде покривала на главу сваког раста да лове душе. Ловите душе мог народа, а своје ли ћете душе сачувати?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
И скврните ме код народа мог за грст јечма и за залогај хлеба убијајући душе, које не би требало да умру, и чувајући у животу душе које не треба да живе, лажући народу мом, који слуша лаж.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
Зато овако вели Господ Господ: Ево мене на ваша узглавља, на која ловите душе да вам долећу, и подераћу их испод лаката ваших, и пустићу душе које ловите да вам долећу.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
И подераћу покривала ваша и избавићу свој народ из ваших руку, и неће више бити у вашим рукама да вам буду лов, и познаћете да сам ја Господ.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Јер жалостисте лажју срце праведнику, ког ја не ожалостих, и креписте руке безбожнику да се не врати са свог злог пута да се сачува у животу.
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Зато нећете виђати таштине и нећете више гатати, него ћу избавити народ свој из ваших руку, и познаћете да сам ја Господ.