< Ezekiyel 13 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A palavra de Javé veio a mim, dizendo:
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
“Filho do homem, profetiza contra os profetas de Israel que profetizam, e diz àqueles que profetizam do próprio coração: 'Ouçam a palavra de Javé:
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
O Senhor Javé diz: “Ai dos profetas insensatos, que seguem seu próprio espírito e não viram nada!
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Israel, seus profetas têm sido como raposas nos lugares de desperdício.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Você não subiu nas brechas ou construiu o muro para a casa de Israel, para permanecer na batalha no tempo de Iavé.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Eles viram falsidade e adivinhação mentirosa, que dizem: 'Javé diz;' mas Javé não os enviou. Eles fizeram os homens esperarem que a palavra fosse confirmada.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Você não viu uma visão falsa, e não falou uma adivinhação mentirosa, na qual você diz, 'Yahweh diz;' mas eu não falei?”.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
“'Portanto, o Senhor Javé diz: “Porque falastes falsidade e vistes mentiras, portanto, eis que eu estou contra vós”, diz o Senhor Javé.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
“Minha mão será contra os profetas que vêem falsas visões e que proferem adivinhações mentirosas”. Eles não estarão no concílio do meu povo, nem serão escritos nos escritos da casa de Israel, nem entrarão na terra de Israel”. Então vocês saberão que eu sou o Senhor Javé”.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
“'Porque, mesmo porque eles seduziram meu povo, dizendo: “Paz”; e não há paz. Quando se constrói um muro, eis que eles o rebocam com cal.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Diga aos que a rebocam com cal que ela cairá. Haverá uma chuva transbordante; e vocês, grandes pedras de granizo, cairão. Um vento tempestuoso vai rasgá-lo.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
Quando o muro tiver caído, não lhe será dito: “Onde está o gesso com o qual você o rebocou?
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
“'Portanto, o Senhor Javé diz: “Eu vou até rasgá-lo com um vento tempestuoso em minha ira. Haverá uma chuva transbordante em minha ira, e grandes pedras de granizo na ira para consumi-la”.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Por isso, derrubarei a parede que vocês rebocaram com cal e a derrubarei, para que seus alicerces sejam descobertos”. Ela cairá, e você será consumido no meio dela. Então você saberá que eu sou Yahweh.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
Thus Realizarei minha ira sobre a parede, e sobre aqueles que a rebocaram com cal. Eu lhes direi: 'O muro não é mais, nem aqueles que o rebocaram -
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
a saber, os profetas de Israel que profetizam a respeito de Jerusalém, e que vêem visões de paz para ela, e não há paz'”, diz o Senhor Javé”.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
Você, filho do homem, põe seu rosto contra as filhas de seu povo, que profetizam do próprio coração; e profetiza contra elas,
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
e diz: “O Senhor Javé diz: 'Ai das mulheres que cosem fitas mágicas em todos os cotovelos e fazem véus para a cabeça das pessoas de toda estatura para caçar almas! Vocês caçarão as almas do meu povo e salvarão as almas vivas para vocês mesmos?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
Vocês me profanaram entre meu povo por punhados de cevada e por pedaços de pão, para matar as almas que não deveriam morrer e para salvar as almas vivas que não deveriam viver, por suas mentiras ao meu povo que escuta as mentiras”.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
“Portanto, o Senhor Javé diz: 'Eis que eu sou contra suas faixas mágicas, com as quais você caça as almas para fazê-las voar, e eu as arrancarei de seus braços'. Deixarei as almas voar livres, até mesmo as almas que vocês ludibriarem como pássaros”.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
Também rasgarei seus véus e livrarei meu povo de suas mãos; e eles não estarão mais em suas mãos para serem ludibriados. Então você saberá que eu sou Yahweh.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Porque com a mentira afligistes o coração do justo, que eu não entristeci; e fortalecestes as mãos do ímpio, para que ele não voltasse de seu mau caminho, e fosse salvo vivo.
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Portanto, não vereis mais falsas visões nem praticareis adivinhações. Eu livrarei meu povo de suas mãos. Então você saberá que eu sou Yahweh”.

< Ezekiyel 13 >