< Ezekiyel 13 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
خداوند با من سخن گفت و فرمود: «ای پسر انسان، کلام مرا بر ضد انبیای دروغین اسرائیل اعلام نما، بر ضد انبیایی که افکار خود را به عنوان پیغام من بیان می‌کنند.»
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
خداوند یهوه فرمود: «وای بر انبیای نادانی که خیالات خود را به جای کلام من بازگو می‌کنند، حال آنکه هیچ کلامی از جانب من بر ایشان نازل نشده است.
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
«ای مردم اسرائیل، انبیای شما مانند روباهانی در خرابه‌ها هستند. ایشان هیچ نفعی به شما نرسانده‌اند.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
آنان هیچگاه خرابیهای حصار شهر را تعمیر نکردند تا بتوانید در آن روزی که خداوند مقرر کرده، در برابر دشمن بایستید.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
رؤیاهای ایشان باطل است و پیشگویی‌هایشان دروغ! می‌گویند که پیغامشان از جانب من است، در حالی که من ایشان را نفرستاده‌ام. با وجود این، انتظار دارند که پیشگویی‌هایشان عملی شوند!
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
ای پیام‌آوران دروغین، رؤیاها و پیامهایتان، همه دروغ است! می‌گویید که آنها از طرف من می‌باشد، در حالی که من هیچگاه با شما سخن نگفته‌ام!»
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
از این رو خداوند یهوه می‌فرماید: «به سبب این رؤیاهای ساختگی و این دروغها، من بر ضد شما هستم،
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
و شما را مجازات خواهم نمود و از میان رهبران اسرائیل ریشه‌کن خواهم ساخت. نام شما را از دفتر خاندان اسرائیل پاک خواهم نمود و هیچ‌یک از شما به سرزمین اسرائیل باز نخواهد گشت، تا بدانید که من خداوند یهوه هستم.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
«این مردان شریر، قوم مرا فریب داده، می‌گویند که همه چیز در امن و امان است، حال آنکه چنین نیست. قوم من دیواری سست می‌سازند و این پیام‌آوران دروغگو نیز تشویقشان می‌نمایند و با گچ، آن دیوار را سفید می‌کنند.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
پس به این معمارها بگو که دیوارشان فرو خواهد ریخت. بارانی سیل‌آسا خواهم بارانید، تگرگی سخت خواهم آورد و طوفانی شدید خواهم فرستاد تا آن را ویران سازند؛
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
و آن هنگام که دیوار فرو افتد، مردم بر سر ایشان فریاد خواهند زد: «چرا به ما نگفتید که دیوار سست و ناپایدار است؟ چرا روی آن را گچ گرفتید و معایبش را پوشانیدید؟»
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
بله، با طوفان عظیم خشم، با تگرگ و باران غضب خود، آن را از جا کنده، نابودش خواهم نمود.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
دیوار گچکاری شدهٔ ایشان خراب و با خاک یکسان خواهد شد و بر سرشان فرو خواهد ریخت و در زیر آن له خواهند شد، تا بدانند که من خداوند یهوه هستم.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
زمانی که خشم من بر ضد این دیوار و معمارانش پایان یابد، اعلام خواهم کرد که نه دیواری مانده و نه معماری؛
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
زیرا معمارانش، انبیای دروغگویی بودند که می‌گفتند اورشلیم در امان خواهد بود، در حالی که چنین نبود.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
«حال ای پسر انسان، کلام مرا بر ضد زنانی که افکار خود را به جای پیام من بیان می‌کنند، اعلام نما.»
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
خداوند یهوه فرمود که به ایشان چنین بگویم: «وای بر شما که قوم مرا گمراه می‌کنید. به بازوهایشان طلسم و جادو می‌بندید و دستار افسون به آنها می‌فروشید تا بتوانند اختیار زندگی دیگران را به دست بگیرند. آیا می‌خواهید اختیار مرگ و زندگی قوم مرا در دست داشته باشید تا جیبتان را پر کنید؟
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
برای مشتی جو و چند لقمه نان، قومم را از من دور می‌سازید. کسانی را که باید زنده بمانند، به کشتن می‌دهید و آنانی را که نباید زنده بمانند، زنده نگه می‌دارید. به این ترتیب به قوم من دروغ می‌گویید و آنها نیز باور می‌کنند.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
«از این رو من بر ضد سحر و جادوی شما هستم که با آنها زندگی افراد قوم مرا طلسم کرده‌اید و مانند پرنده‌ای به دام انداخته‌اید. طلسمهای شما را باطل کرده، دعاهایتان را بی‌اثر خواهم ساخت و قوم خود را از دام شما رهایی خواهم بخشید.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
دستارهای افسون را خواهم درید و قومم را از چنگ شما نجات خواهم بخشید. ایشان دیگر در دام شما نخواهند بود تا بدانید که من یهوه هستم.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
شما با دروغهای خود، مردم درستکار را برخلاف میل من، دل شکسته و دردمند ساخته‌اید، ولی افراد شرور را تشویق کرده‌اید و باعث شده‌اید آنها از راههای گناه‌آلودشان توبه نکنند و رستگار نشوند.
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
اما از این پس، دیگر رؤیاهای باطل نخواهید دید و غیبگویی‌های گمراه کننده نخواهید کرد، زیرا من قوم خود را از نفوذ قدرت شما رهایی خواهم داد تا بدانید که من یهوه هستم!»

< Ezekiyel 13 >