< Ezekiyel 13 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ilizwi likaThixo lafika kimi lisithi:
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
“Ndodana yomuntu, phrofitha umelana labaphrofethi bako-Israyeli abaphrofethayo khathesi. Uthi kulabo abaphrofetha okuvela emicabangweni yabo: ‘Zwanini ilizwi likaThixo!
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
Nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Maye kubaphrofethi abayizithutha abalandela umoya wabo kodwa bengabonanga lutho!
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Abaphrofethi bakho, we Israyeli, banjengamakhanka asemanxiweni.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Kawuyanga phezulu ezikhexeni emdulini ukuba uwulungisele indlu ka-Israyeli ukuze uqine empini ngosuku lukaThixo.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Imibono yabo iyinkohliso njalo lobungoma babo bungamanga. Bathi, “uThixo uthi,” yena uThixo engabathumanga; kodwa bathembe ukuthi amazwi abo azagcwaliseka.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Kalikayiboni imibono yenkohliso na, njalo lakhuluma ubungoma bamanga lapho lisithi, “uThixo uthi,” lanxa mina ngingatshongo?
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Ngakho-ke nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Ngenxa yamazwi enu enkohliso kanye lemibono yenu yamanga, ngimelana lani, kutsho uThixo Wobukhosi.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Isandla sami sizamelana labaphrofethi ababona imibono yenkohliso bakhulume ubungoma bamanga. Kabayikuba ngabenhlangano yabantu bami kumbe balotshwe emibhalweni yendlu ka-Israyeli, loba bangene elizweni lako-Israyeli. Lapho-ke lizakwazi ukuthi nginguThixo Wobukhosi.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
Ngenxa yokuthi bedukisa abantu bami, besithi “Ukuthula,” khona ukuthula kungekho, njalo ngoba, nxa kwakhiwe umduli ongaqinanga, bayawubhada ngekalaga,
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
ngakho tshela labo abawubhada ngekalaga ukuthi uzadilika. Kuzakuza isihlambi sezulu, njalo ngizaletha isiqhotho esitshaya phansi, kuqhamuke umoya olamandla.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
Lapho umduli udilika, abantu kabayikulibuza na bathi, “Ingaphi ikalaga elawubhada ngayo?”
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Ngakho-ke nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Ngolaka lwami ngizadedela umoya olamandla, kuthi ngokuthukuthela kwami isiqhotho lesihlambi sezulu kune ngentukuthelo ebhubhisayo.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Ngizadiliza umduli eliwubhade ngekalaga ngiwuwisele phansi ukuze isisekelo sawo sibe segcekeni. Nxa ususiwa lizafela kuwo; njalo lizakwazi ukuthi nginguThixo.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
Ngakho ngizachitha ulaka lwami ngimelane lomduli kanye lalabo abawubhada ngekalaga. Ngizakuthi kini, “Umduli kawusekho njalo yiso leso lakulabo abawucomba ngekalaga,
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
labobaphrofethi bako-Israyeli abaphrofetha ngeJerusalema babona imibono yokuthula ngalo, khona ukuthula kungekho, kutsho uThixo Wobukhosi.”’
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
Khathesi-ke ndodana yomuntu, melana lamadodakazi abantu bakini aphrofetha okwemicabango yawo. Phrofetha umelana lawo
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
uthi, ‘Nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Maye kwabesifazane abathungela intebe ezihlakaleni zabo zonke benze lezimbombozo zamakhanda abo ezilobude obehlukeneyo ukuze bathiye abantu. Lizathiya impilo yabantu bami kodwa lilondoloze eyenu na?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
Lingithukile phakathi kwabantu bami ngenxa yohetshezana lwebhali kanye lemvuthuluka yesinkwa. Ngokuqamba amanga ebantwini bami, abawalalelayo amanga, selibabulele labo ababengamelanga bafe, kodwa layekela abangafanelanga ukuphila.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
Ngakho nanku okutshiwo nguThixo Wobukhosi: Ngimelana lezintebe zenu elithiya abantu ngazo njengenyoni njalo ngizazidabula ezingalweni zenu; ngizabakhulula abantu elibathiya njengenyoni.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
Izimbombozo zenu ngizazidabula ngikhulule abantu bami ezandleni zenu, njalo kabayikuba ngaphansi kwamandla okubazingela kwenu. Lapho-ke lizakwazi ukuthi nginguThixo.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Ngenxa yokuthi lenyelisa inhliziyo zabalungileyo ngamanga enu, lapho ngangingabalethelanga sizi, njalo ngoba lakhuthaza ababi ukuba bangaphenduki ezindleleni zabo ezimbi ngalokho basilise ukuphila kwabo,
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
ngakho kaliyikubona imibono yamanga futhi loba izenzo zobungoma. Abantu bami ngizabahlenga ezandleni zenu. Lapho-ke lizakwazi ukuthi nginguThixo.’”

< Ezekiyel 13 >