< Ezekiyel 13 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Éternel me fut adressée en ces mots:
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
Fils de l'homme, prophétise contre les prophètes d'Israël qui prophétisent, et dis à ceux qui prophétisent d'après leurs sentiments propres: Écoutez la parole de l'Éternel!
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Malheur aux prophètes insensés qui suivent leur esprit propre, et ne voient rien!
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Tels des renards dans des ruines, tels sont tes prophètes, Israël.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Vous ne montez pas à la brèche, et n'élevez point de mur autour de la maison d'Israël, afin de tenir ferme dans le combat à la journée de l'Éternel.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Ils ont des visions trompeuses, et des présages menteurs, ceux qui disent: « L'Éternel a dit, » tandis que l'Éternel ne les a point envoyés; et qui font espérer les effets de leur parole.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Vos visions ne sont-elles pas trompeuses, et vos présages menteurs, quand vous dites: « L'Éternel a dit, » tandis que je n'ai point parlé?
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Aussi, ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Parce que vos discours sont trompeurs et vos visions des mensonges, pour cela, c'est à vous que j'en veux, dit le Seigneur, l'Éternel.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Et je ferai sentir ma main aux prophètes dont les visions sont trompeuses et les présages menteurs. Ils ne seront point associés à mon peuple, ni inscrits au rôle de la maison d'Israël, ni introduits au pays d'Israël, afin que vous sachiez que je suis le Seigneur, l'Éternel;
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
eparce que, oui, parce qu'ils égarent mon peuple en disant: Salut! tandis qu'il n'y a point de salut, et que, s'il élève un mur, eux ils le recouvrent de plâtre.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Dis à ceux qui replâtrent, qu'il s'écroulera: il pleuvra par torrents, et vous, pierres de la grêle, vous tomberez et le vent des tempêtes éclatera.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
Et voici, le mur croulera. Ne vous dira-t-on pas: Où est le plâtre dont vous l'avez recouvert?
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Aussi, ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Dans ma fureur je ferai éclater le vent des tempêtes, et dans ma colère la pluie viendra par torrents, avec les pierres de la grêle dans mon courroux, afin de détruire.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Et je ferai crouler le mur que vous recouvrîtes de plâtre, et je le coucherai par terre, et ses fondements seront mis à nu; il est tombé et vous périssez sous ses ruines, afin que vous sachiez que je suis l'Éternel.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
Et ainsi j'assouvirai ma fureur sur ce mur et sur ceux qui le recouvrent de plâtre; puis je vous dirai: Le mur n'est plus; ils ne sont plus ceux qui le replâtraient,
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
les prophètes d'Israël, qui prophétisent à Jérusalem, et dont les visions lui présagent le salut, tandis qu'il n'y a pas de salut, dit le Seigneur, l'Éternel.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
Et toi, fils de l'homme, tourne tes regards du côté des filles de ton peuple qui prophétisent d'après leur sentiment propre, et prophétise contre elles!
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
et dis: Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Malheur à vous qui cousez des coussinets pour toutes les jointures de la main, et faites des oreillers pour les têtes de toutes les tailles, pour prendre les âmes au piège! Penseriez-vous prendre au piège les âmes de mon peuple, et conserver la vie aux vôtres?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
Vous me déshonorez auprès de mon peuple pour quelques poignées d'orge et pour quelques bouchées de pain, en annonçant la mort aux âmes qui ne doivent pas mourir, et la vie aux âmes qui ne doivent pas vivre; en trompant mon peuple qui prête l'oreille au mensonge. Aussi, ainsi parle le Seigneur, l'Éternel:
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
Voici, je m'attaque à vos oreillers où vous prenez les âmes au piège, afin qu'elles s'envolent, et je les arracherai de vos bras, et je dégagerai les âmes que vous prenez au piège, afin qu'elles s'envolent.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
Et je mettrai vos oreillers en pièces, et je tirerai mon peuple de vos mains, afin qu'il ne soit plus une proie entre vos mains et que vous sachiez que je suis l'Éternel.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Parce que vous affligez le cœur du juste par le mensonge, quand moi-même je ne l'ai pas affligé, et parce que vous fortifiez le méchant dans ce qu'il fait, en sorte qu'il ne quitte pas sa mauvaise voie pour obtenir la vie,
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
à cause de cela, vous n'aurez plus vos visions mensongères et vous ne ferez plus de prédictions, et je tirerai mon peuple de vos mains, afin que vous sachiez que je suis l'Éternel.