< Ezekiyel 13 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
and he seide, Sone of man, profesie thou to the profetis of Israel that profesien; and thou schalt seie to hem that profesien of her herte,
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
Here ye the word of the Lord. The Lord God seith these thingis, Wo to the vnwise profetis, that suen her spirit, and seen no thing;
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Israel, thi profetis weren as foxis in desert.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Ye stieden not euene ayens, nether ayensettiden a wal for the hous of Israel, that ye shulden stonde in batel in the dai of the Lord.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Thei seen veyn thingis, and deuynen a leesyng, and seien, The Lord seith, whanne the Lord sente not hem; and thei contynueden to conferme the word.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Whether ye seen not a veyn visioun, and spaken fals diuynyng, and seiden, The Lord seith, whanne Y spak not?
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Therfor the Lord God seith these thingis, For ye spaken veyn thingis, and sien a leesyng, therfor lo! Y to you, seith the Lord God.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And myn hond schal be on the profetis that seen veyn thingis, and dyuynen a leesyng; thei schulen not be in the councel of my puple, and thei schulen not be writun in the scripture of the hous of Israel, nether thei schulen entre in to the lond of Israel; and ye schulen wite, that Y am the Lord God.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
For thei disseyueden my puple, and seiden, Pees, pees, and no pees is; and it bildide a wal, but thei pargitiden it with fen with out chaffis.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Seie thou to hem that pargiten with out temperure, that it schal falle doun; for a strong reyn schal be flowynge, and I shal yyue ful grete stoones fallinge fro aboue, and Y schal yyue a wynd of tempest that distrieth.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
For lo! the wal felle doun. Whether it schal not be seid to you, Where is the pargetyng, which ye pargetiden?
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Therfor the Lord God seith these thingis, And Y schal make the spirit of tempestis to breke out in myn indignacioun, and strong reyn flowynge in my strong veniaunce schal be, and greet stoonys in wraththe in to wastyng.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And Y schal distrie the wal, which ye pargetiden with out temperure, and Y schal make it euene with the erthe; and the foundement therof schal be schewid, and it schal falle doun, and it schal be wastid in the myddis therof; and ye schulen wite, that Y am the Lord.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
And Y schal fille myn indignacioun in the wal, and in hem that pargeten it with out temperure; and Y schal seie to you, The wal is not, and thei ben not,
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
that pargeten it, the profetis of Israel, that profesien to Jerusalem, and seen to it the visioun of pees, and pees is not, seith the Lord God.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
And thou, sone of man, sette thi face ayens the douytris of thi puple, that profesien of her herte; and profesie thou on hem,
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
and seie thou, The Lord God seith these thingis, Wo to hem that sowen togidere cuschens vndur ech cubit of hond, and maken pilewis vndur the heed of ech age, to take soulis; and whanne thei disseyueden the soulis of my puple, thei quykenyden the soulis of hem.
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
And thei defouliden me to my puple, for an handful of barli, and for a gobet of breed, that thei schulden sle soulis that dien not, and quykene soulis that lyuen not; and thei lieden to my puple, bileuynge to leesyngis.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
For this thing the Lord God seith these thingis, Lo! Y to youre cuschens, bi whiche ye disseyuen soulis fliynge; and Y schal al to-breke tho fro youre armes, and Y schal delyuere soulis which ye disseyuen, soulis to fle.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
And Y schal al to-breke youre pilewis, and Y schal delyuere my puple fro youre hond; and thei schulen no more be in youre hondis, to be robbid; and ye schulen wite, that Y am the Lord.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
For that that ye maden falsli the herte of a iust man to morene, whom Y made not sori; and ye coumfortiden the hondis of a wickid man, that he schulde not turne ayen fro his yuel weie, and lyue.
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Therfor ye schulen not se veyn thingis, and ye schulen no more dyuyne false dyuynyngis; and Y schal delyuere my puple fro youre hond, and ye schulen wite, that Y am the Lord.