< Ezekiyel 13 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
“Son of man, you are to prophesy against the prophets of Israel who right now are busy prophesying. Tell those who make up their own prophecies: Listen to the word of the Lord!
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
This is what the Lord God says: Disaster is coming to these foolish prophets who follow their own ideas. They haven't seen anything.
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Israel, your prophets are like foxes that live in the ruins.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
They didn't go and help repair the gaps in the wall that defends the people of Israel so that it would stand secure during the battle on the Day of the Lord.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
The visions they see are false, and the prophecies they give are lies. They claim, ‘This is what the Lord says,’ when the Lord didn't send them. Even so they still expect their message to be fulfilled!
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Isn't it a false vision that you people saw? Isn't it a prophecy of lies when you announce, ‘This is what the Lord says,’ even though I haven't said anything?
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
So this is what the Lord God says: Since you've spoken lies and claimed to see false visions, then watch out, because I'm against you, declares the Lord God.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
I will punish the prophets who see false visions and give prophecies that are lies. They will not belong to the assembly of my people or be listed in the register of Israelites, and they won't be allowed to enter the country of Israel. Then you will know that I am the Lord God.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
They have deceived my people by saying, ‘We shall have peace,’ when there won't be any peace. It's like they're putting a coat of whitewash on an unstable wall of loose stones that the people have built.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
So tell those people whitewashing the wall that it's going to collapse. Rain will come pouring down. I will send hailstones crashing down on it. A windstorm will blow hard against it.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
Don't you think that when the wall collapses people are going to ask you, ‘What happened to the whitewash you painted it with?’
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
So this is what the Lord God says: In my furious anger I'm going to send a windstorm, pouring rain, and hailstones to destroy the wall.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
I will demolish the wall you whitewashed, knocking it to the ground to reveal its foundations. The city is going to fall, and you're going to be destroyed with it. Then you will know that I am the Lord.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
Once the wall and those who whitewashed it have experienced my anger, I will tell you: The wall is no more, and those who whitewashed it are no more,
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
those ‘prophets’ of Israel who prophesied to Jerusalem and claimed to have seen a vision of peace for her when there wasn't going to be any peace, declares the Lord God.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
Now, son of man, you are to oppose those Israelite women who make up prophecies in their own minds. Prophesy against them
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
and tell them that this is what the Lord God says: Disaster is coming to the women who sew bracelets of magic charms for their wrists and make veils for all kinds of people to wear as ways to trap and exploit them. Do you think you can trap the lives of my people yet still keep your own?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
You have disgraced me among my people for a few handfuls of barley and scraps of bread. By lying to my people who believe in you, you have killed those who shouldn't have died and let others live who shouldn't.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
So this is what the Lord God says: Watch out! I condemn the magic charms you use to trap people like birds, and I will rip them off your arms. I will set free those you have trapped.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
I will also rip off your veils and rescue my people from your power, so that they will no longer be your victims. Then you will know that I am the Lord.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Because you have discouraged good people with your lies, even though I didn't have anything against them, and because you have encouraged the wicked that they shouldn't give up from their evil ways to save their lives,
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
from now on you won't claim these false visions or practice magic. I will rescue my people from your power. Then you will know that I am the Lord.”

< Ezekiyel 13 >