< Ezekiyel 13 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
I opet mi dođe riječ Jahvina:
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
“Sine čovječji! Prorokuj protiv onih koji se grade prorocima u Izraelu!
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
Reci tim prorocima koji prorokuju po svojoj glavi: 'Čujte riječ Jahvinu! Ovako govori Jahve Gospod: Jao prorocima bezumnim koji duh svoj slijede a ništa ne vide!
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Ti su tvoji proroci, Izraele, kao lisice usred ruševina.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
Vi se ne popeste na proboje i ne zidaste zida oko doma Izraelova da se održi u boju u dan Jahvin.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
Viđenja su njihova isprazna, i lažna su njihova proricanja. Govore 'Riječ Jahvina!' - a Jahve ih nije poslao. I još očekuju da će im se riječi ispuniti.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Zar ne vidite da su vam viđenja isprazna i da su vam lažna proricanja kad govorite 'Riječ Jahvina!' - a ja nisam govorio.'
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Stoga ovako govori Jahve Gospod: 'Zato što govorite isprazno i laž vidite, evo me protiv vas' - riječ je Jahve Gospoda!
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Evo, ruka moja bit će protiv proroka koji vide isprazno i laž proriču: neće više biti u zboru mojega naroda, neće biti upisani u knjigu doma Izraelova, nikad više neće stupiti na tlo Izraelovo! I znat će da sam ja Jahve Gospod!
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
Jer narod moj obmanjuju govoreći 'Mir' kad mira nema. I dok jedni hoće da se zid utvrdi, oni hoće da se samo ožbuka.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Reci onima koji hoće da se samo ožbuka: 'Past će!' Udarit će silan pljusak, oborit ću na nj grÓad kao kamenje, bjesnjet će olujni vihori.
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
Evo, zid će pasti! Neće li vas tada pitati: 'Gdje vam je sada žbuka kojom ste ga ožbukali?'
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Zato ovako govori Jahve Gospod: 'U svojoj jarosti razbjesnit ću olujne vihore, u srdžbi ću svojoj udariti silnim pljuskom da ga zatrem, u gnjevu ću na nj oboriti grÓad kao kamenje.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Obalit ću zid što ga vi žbukom ožbukaste, na zemlju ću ga oboriti da mu se razgole temelji. Past će zid, i vi ćete pod njim izginuti! Tada ćete znati da sam ja Jahve!
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
Tako ću iskaliti gnjev nad zidom i nad onima koji ga žbukom ožbukaše. A vama ću reći: Nema više zida! Nema onih koji ga žbukom ožbukaše.
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
Nema izraelskih proroka koji Jeruzalemu proricahu i koji mu mir vidješe kad mira ne bijaše.' Tako govori Jahve Gospod.”
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
“Sine čovječji, okreni lice protiv kćeri svojega naroda koje prorokuju po svojoj glavi! Prorokuj protiv njih:
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
Ovako govori Jahve Gospod: 'Jao onima koje vezu poveze za svačije ruke i koje prave prijevjese za glave svake veličine da ulove duše! Mislite li uloviti sve duše mojega naroda a svoje duše sačuvati žive?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
Obeščašćujete me pred mojim narodom za šaku ječma, za zalogaj kruha, ubijajući duše koje ne bi trebale da umru, a spasavajući one koje ne bi trebale da žive; i obmanjujete tako narod moj koji rado sluša vaše laži.'
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
Zato ovako govori Jahve Gospod: 'Evo me protiv vaših poveza kojima lovite duše kao ptice! Rastrgat ću sve to na vašim rukama i oslobodit ću duše koje time hvatate kao ptice!
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
Poderat ću vaše prijevjese i oslobodit ću svoj narod da ne bude više plijen vaših ruku. I znat ćete da sam ja Jahve!
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Jer vi lažju ražalostiste srce pravednika, koje ja ražalostiti ne htjedoh, a okrijepiste ruke bezbožnika da se ne obrati od zla puta bezbožničkog pa da život spasi.
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Zato nećete više vidjeti isprazno niti ćete laž proricati: ja ću osloboditi narod svoj iz vaših ruku. I znat ćete da sam ja Jahve!'”