< Ezekiyel 12 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
RAB bana şöyle seslendi:
2 ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
“İnsanoğlu, asi bir halkın arasında yaşıyorsun. Gözleri varken görmüyor, kulakları varken işitmiyorlar. Çünkü bu halk asidir.
3 “Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
“Sen, insanoğlu, sürgüne gidecekmiş gibi eşyanı topla, onların gözü önünde, gündüzün yola çık, bulunduğun yerden başka bir yere git. Kim bilir, asi bir halk olmalarına karşın seni görüp anlayabilirler.
4 Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
Gündüzün, halkın gözü önünde topladığın sürgün eşyanı çıkar. Akşam yine onların gözü önünde sürgüne giden biri gibi yola çık.
5 Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
Onlar seni izlerken duvarı delip eşyanı çıkar.
6 Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
Seni izlerlerken eşyanı sırtlayıp karanlıkta taşı. Ülkeyi görmemek için yüzünü ört. Çünkü yapacakların İsrail halkı için bir uyarı olacaktır.”
7 Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
Bana verilen buyruk uyarınca davrandım. Gündüzün sürgüne gidecekmiş gibi eşyalarımı çıkardım. Akşam elimle duvarı deldim. Eşyalarımı karanlıkta çıkarıp onlar izlerken sırtımda taşıdım.
8 Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ertesi sabah RAB bana seslendi:
9 “Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
“İnsanoğlu, o asi İsrail halkı sana, ‘Ne yapıyorsun?’ diye sormadı mı?
10 “Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
“Onlara de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Yeruşalim'deki önder ve orada yaşayan bütün İsrail halkına ilişkin bir bildiridir bu.
11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
Ben sizin için bir uyarıyım’ de. Sana yaptığımın tıpkısı onlara da yapılacak. Tutsak olarak sürgüne gidecekler.
12 “Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
“Onların önderi karanlıkta eşyasını sırtında taşıyarak yola koyulacak. Eşyasını çıkarmak için duvarda bir gedik açacak. Ülkeyi görmemek için yüzünü örtecek.
13 Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
Onun üzerine ağımı atacağım, kurduğum tuzağa düşecek. Onu Babil'e, Kildan ülkesine götüreceğim, ama ülkeyi göremeden orada ölecek.
14 Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
Çevresindekilerin tümünü –yardımcılarını, ordusunu– dünyanın dört bucağına dağıtacağım. Yalın kılıç onların peşlerine düşeceğim.
15 “Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
Onları uluslar arasına dağıtıp ülkelere sürdüğümde, benim RAB olduğumu anlayacaklar.
16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
Gittikleri uluslarda yaptıkları bütün iğrenç uygulamaları anlatmaları için aralarından birkaç kişiyi kılıçtan, kıtlıktan, salgın hastalıktan sağ bırakacağım. Böylece benim RAB olduğumu anlayacaklar.”
17 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
18 “Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
“İnsanoğlu, yiyeceğini titreyerek ye, suyunu korkudan ürpererek iç.
19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
Ülkede yaşayan halka de ki, ‘Egemen RAB İsrail ve Yeruşalim'de yaşayanlar için şöyle diyor: Yiyeceklerini umutsuzluk içinde yiyecek, sularını şaşkınlık içinde içecekler. Orada yaşayanların yaptığı zorbalık yüzünden ülke ıssız bırakılacak.
20 Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Halkın içinde yaşadığı kentler yakılacak, ülke çöle dönüşecek. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız.’”
21 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
22 “Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
“İnsanoğlu, İsrail'de yaygın olan, ‘Günler geçiyor, her görüm boşa çıkıyor’ deyişinin anlamı nedir?
23 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
Onlara de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Ben bu deyişe son vereceğim. Bundan böyle İsrail'de bir daha söylenmeyecek.’ Yine onlara de ki, ‘Her görümün yerine geleceği günler yaklaştı.
24 Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
Artık İsrail halkı arasında yalan görüm ya da aldatıcı falcılık olmayacak.
25 Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Ama ben RAB, ne dersem gecikmeden olacak. Siz, ey asi İsrail halkı, söylediklerimin tümünü sizin günlerinizde yerine getireceğim. Böyle diyor Egemen RAB.’”
26 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
27 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
“İnsanoğlu, İsrail halkı, ‘Onun gördüğü görüm uzak günler için, peygamberlik sözleri de uzak gelecekle ilgili’ diyor.
28 “Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
“Bundan ötürü onlara de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Söylediğim sözlerden hiçbiri artık gecikmeyecek, ne dersem olacak. Böyle diyor Egemen RAB.’”