< Ezekiyel 12 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۱
2 ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
«ای پسر انسان تو در میان خاندان فتنه انگیز ساکن می‌باشی که ایشان را چشمها به جهت دیدن هست اما نمی بینند و ایشان را گوشهابه جهت شنیدن هست اما نمی شنوند، چونکه خاندان فتنه انگیز می‌باشند.۲
3 “Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
اما تو‌ای پسر انسان اسباب جلای وطن را برای خود مهیا ساز. و درنظر ایشان در وقت روز کوچ کن و از مکان خود به مکان دیگر به حضور ایشان نقل کن، شایدبفهمند. اگرچه خاندان فتنه انگیز می‌باشند.۳
4 Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
واسباب خود را مثل اسباب جلای وطن در وقت روز به نظر ایشان بیرون آور. و شامگاهان مثل کسانی که برای جلای وطن بیرون می‌روند بیرون شو.۴
5 Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
و شکافی برای خود در دیوار به حضورایشان کرده، از آن بیرون ببر.۵
6 Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
و در حضور ایشان آن را بر دوش خود بگذار و در تاریکی بیرون ببر وروی خود را بپوشان تا زمین را نبینی. زیرا که تو راعلامتی برای خاندان اسرائیل قرار داده‌ام.»۶
7 Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
پس به نهجی که مامور شدم، عمل نمودم واسباب خود را مثل اسباب جلای وطن در وقت روز بیرون آوردم. و شبانگاه شکافی برای خود به‌دست خویش در دیوار کردم و آن را در تاریکی بیرون برده، به حضور ایشان بر دوش برداشتم.۷
8 Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
وبامدادان کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۸
9 “Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
«ای پسر انسان، آیا خاندان اسرائیل یعنی‌این خاندان فتنه انگیز به تو نگفتند: این چه‌کار است که می‌کنی؟۹
10 “Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
پس به ایشان بگو خداوند یهوه چنین می‌گوید: این وحی اشاره به رئیسی است که دراورشلیم می‌باشد و به تمامی خاندان اسرائیل که ایشان در میان آنها می‌باشند۱۰
11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
بگو: من علامت برای شما هستم. به نهجی که من عمل نمودم، همچنان به ایشان کرده خواهد شد و جلای وطن شده، به اسیری خواهند رفت.۱۱
12 “Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
و رئیسی که درمیان ایشان است (اسباب خود را) در تاریکی بردوش نهاده، بیرون خواهد رفت. و شکافی دردیوار خواهند کرد تا از آن بیرون ببرند. و او روی خود را خواهد پوشانید تا زمین را به چشمان خودنبیند.۱۲
13 Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
و من دام خود را بر او خواهم گسترانید ودر کمند من گرفتار خواهد شد. و او را به بابل به زمین کلدانیان خواهم برد و اگرچه در آنجاخواهد مرد، ولی آن را نخواهد دید.۱۳
14 Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
و جمیع مجاوران و معاونانش و تمامی لشکر او را بسوی هر باد پراکنده ساخته، شمشیری در عقب ایشان برهنه خواهم ساخت.۱۴
15 “Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
و چون ایشان را در میان امت‌ها پراکنده ساخته و ایشان را در میان کشورهامتفرق نموده باشم، آنگاه خواهند دانست که من یهوه هستم.۱۵
16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
لیکن عدد قلیلی از میان ایشان ازشمشیر و قحط و وبا باقی خواهم گذاشت تا همه رجاسات خود را در میان امت هایی که به آنهامی روند، بیان نمایند. پس خواهند دانست که من یهوه هستم.»۱۶
17 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۱۷
18 “Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
«ای پسر انسان! نان خود را با ارتعاش بخور وآب خویش را با لرزه و اضطراب بنوش.۱۸
19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
و به اهل زمین بگو خداوند یهوه درباره سکنه اورشلیم و اهل زمین اسرائیل چنین می‌فرماید: که نان خودرا با اضطراب خواهند خورد و آب خود را باحیرت خواهند نوشید. زیرا که زمین آنها به‌سبب ظلم جمیع ساکنانش از هر‌چه در آن است تهی خواهد شد.۱۹
20 Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
و شهرهای مسکون ایشان خراب شده، زمین ویران خواهد شد. پس خواهیددانست که من یهوه هستم.»۲۰
21 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۲۱
22 “Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
«ای پسر انسان این مثل شما چیست که درزمین اسرائیل می‌زنید و می‌گویید: ایام طویل می‌شود و هر رویا باطل می‌گردد.۲۲
23 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
لهذا به ایشان بگو، خداوند یهوه چنین می‌گوید: این مثل را باطل خواهم ساخت و آن را بار دیگر دراسرائیل نخواهند‌آورد. بلکه به ایشان بگو: ایام، نزدیک است و انجام هر رویا، قریب.۲۳
24 Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
زیرا که هیچ‌رویای باطل و غیب گویی تملق‌آمیز در میان خاندان اسرائیل بار دیگر نخواهد بود.۲۴
25 Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
زیرا من که یهوه هستم سخن خواهم گفت و سخنی که من می‌گویم، واقع خواهد شد و بار دیگر تاخیرنخواهد افتاد. زیرا خداوند یهوه می‌گوید: ای خاندان فتنه انگیز در ایام شما سخنی خواهم گفت و آن را به انجام خواهم رسانید.»۲۵
26 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۲۶
27 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
«ای پسر انسان! هان خاندان اسرائیل می‌گویندرویایی که او می‌بیند، به جهت ایام طویل است واو برای زمانهای بعیده نبوت می‌نماید.۲۷
28 “Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
بنابراین به ایشان بگو: خداوند یهوه چنین می‌فرماید که هیچ کلام من بعد از این تاخیرنخواهد افتاد. و خداوند یهوه می‌فرماید: کلامی که من می‌گویم واقع خواهد شد.»۲۸

< Ezekiyel 12 >