< Ezekiyel 12 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
Fils d’un homme, tu habites au milieu d’une maison qui m’exaspère; ils ont des yeux pour voir, et ils ne voient pas; et des oreilles pour entendre, et ils n’entendent pas: parce que c’est une maison qui m’exaspère.
3 “Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
Toi donc, fils d’un homme, fais-toi des meubles de transmigration, et tu émigreras pendant le jour devant eux, mais tu passeras de ton lieu à un autre lieu en leur présence, pour voir si par hasard ils regarderont; parce que c’est une maison qui m’exaspère.
4 Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
Et tu emporteras au dehors tes meubles comme les meubles d’un émigrant, pendant le jour en leur présence; mais toi, tu sortiras le soir devant eux, comme sort un émigrant.
5 Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
Devant leurs yeux perce-toi la muraille, et tu sortiras par cette ouverture.
6 Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
En leur présence tu seras porté sur les épaules, tu seras emporté dans l’obscurité; tu voileras ta face, et tu ne verras pas la terre, parce que je t’ai établi signe pour la maison d’Israël.
7 Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
Je fis donc comme le Seigneur m’avait ordonné; je transportai mes meubles comme les meubles d’un émigrant pendant le jour; et le soir je me perçai la muraille de ma main, et je sortis dans l’obscurité, porté sur les épaules en leur présence.
8 Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée le matin, disant:
9 “Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
Fils d’un homme, est-ce que la maison d’Israël, maison qui m’exaspère, ne t’a pas dit: Que fais-tu?
10 “Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
Dis-leur: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Ce malheur accablant tombera sur le chef qui est dans Jérusalem, et sur toute la maison d’Israël, qui est au milieu d’eux.
11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
Dis: Moi je suis votre signe; comme j’ai fait, ainsi il leur sera fait; ils iront en transmigration et en captivité.
12 “Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
Ce chef qui est au milieu d’eux sera porté sur les épaules; il sortira dans l’obscurité; ils perceront la muraille pour le faire sortir de la ville, sa face sera couverte, afin qu’il ne voie pas de l’œil la terre.
13 Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
Et j’étendrai mon rets sur lui, et il sera pris dans ma seine; et je l’emmènerai à Babylone dans la terre des Chaldéens; et il ne la verra pas, et il y mourra.
14 Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
Et tous ceux qui sont autour de lui, sa garde, ses bataillons, je les disperserai à tout vent, et je tirerai le glaive après eux.
15 “Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
Et ils sauront que je suis le Seigneur, quand je les aurai dispersés parmi les nations, et que je les aurai disséminés dans les divers pays,
16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
Et je laisserai un petit nombre d’entre eux échapper au glaive, à la famine et à la peste, afin qu’ils racontent tous leurs crimes parmi les nations chez lesquelles ils entreront; et ils sauront que je suis le Seigneur.
17 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
18 “Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
Fils d’un homme, mange ton pain dans le trouble; et ton eau, bois-la aussi à la hâte et dans la tristesse.
19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
Et tu diras au peuple du pays: Voici ce que dit le Seigneur Dieu à ceux qui habitent dans Jérusalem, dans la terre d’Israël: Ils mangeront leur pain dans l’inquiétude; leur eau, ils la boiront dans la désolation, afin que cette terre soit dépouillée de sa multitude d’habitants, à cause de l’iniquité de tous ceux qui habitent en elle.
20 Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Et les cités qui sont maintenant habitées seront désolées, et la terre déserte; et vous saurez que je suis le Seigneur.
21 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
22 “Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
Fils d’un homme, quel est ce proverbe qui court parmi vous dans la terre d’Israël,’proverbe de gens disant: Pour longtemps seront différés les jours, et toute vision s’évanouira?
23 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
Pour cela, dis-leur: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Je ferai cesser ce proverbe, et on ne le dira plus publiquement dans Israël; et dis-leur que les jours sont proches, ainsi que la réalisation de toute vision.
24 Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
Car aucune vision ne sera plus vaine, ni aucune divination ambiguë, au milieu des enfants d’Israël.
25 Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Parce que moi le Seigneur je parlerai; et toute parole que j’aurai dite s’accomplira et ne sera pas différée davantage; mais durant vos jours, maison qui m’exaspères, je dirai une parole et je l’exécuterai, dit le Seigneur Dieu.
26 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
27 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
Fils d’un homme, voilà la maison d’Israël disant: La vision que celui-ci voit n’aura son effet que dans bien des jours, et c’est pour des temps éloignés qu’il prophétise.
28 “Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
À cause de cela dis-leur: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Aucune de mes paroles ne sera plus différée; la parole que j’aurai dite s’accomplira, dit le Seigneur Dieu.