< Ezekiyel 12 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
A message from the Lord came to me, saying,
2 ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
“Son of man, you are living among rebellious people. They have eyes to see but they don't see, and ears to hear but they don't hear, because they are rebellious people.
3 “Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
So, son of man, go and pack your bags as if you're going into exile. As people watch, get everything ready during the day so you can leave where you are and go somewhere else. Maybe they will realize what this means, even though they are rebellious people.
4 Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
Take your bags out for traveling into exile during the day while they watch. But you yourself are to leave in the evening as they watch, just like someone going into exile.
5 Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
While they go on watching, knock down part of the wall of your house and take your belongings out through the hole.
6 Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
When it gets dark, as they continue to watch, put your bags on your shoulder and carry them as you leave. Cover your face so that you can't see the country you're leaving behind, because I'm providing you as a sign to warn the people of Israel.”
7 Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
So I did as I was told. I took my bags out to go into exile during the day, and in the evening I knocked down part of the wall of my house with my bare hands. I took my belongings out when it got dark, carrying them on my shoulder while they watched.
8 Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In the morning a message from the Lord came to me, saying,
9 “Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
“Son of man, haven't those rebellious Israelites asked you, ‘What are you doing?’
10 “Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
Tell them that this is what the Lord God says: ‘This prophetic sign concerns the prince who is ruling in Jerusalem and all the people of Israel who are living there.’
11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
You are to say to them, ‘I'm a sign to you.’ Just as it was demonstrated here, so it will happen to them—they will go into exile as prisoners.
12 “Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
When it gets dark, their prince will also put his bags on his shoulder and leave. They will knock down the wall to take him away. He will cover his face so he can't see the country he's leaving behind.
13 Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
But I will catch him in my net; I will trap him in my snare. I will take him to Babylon in the country of Babylonia. However, won't see it, and he'll die there.
14 Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
I'm going to scatter all his attendants and all his troops in every direction, and I will chase after them with a drawn sword.
15 “Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
They will know that I am the Lord when I scatter them among the different nations and countries.
16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
But I will let a few of them survive war, famine, and disease so that they can tell the nations where they're exiled about all their disgusting sins. Then they will know that I am the Lord.”
17 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me, saying,
18 “Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
“Son of man, tremble as you eat your bread; shake with worry as you drink your water.
19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
Then explain to the people of this country that this is what the Lord God says to those living in Jerusalem and in the country of Israel: They will be worried as eat their bread and they will be in despair as they drink their water, for their land will be stripped bare because of the violent crimes committed by everyone who lives there.
20 Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
The towns will be destroyed, and the countryside turned into a wasteland. Then you will know that I am the Lord.”
21 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Another message from the Lord came to me, saying,
22 “Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
“Son of man, what's this proverb you people have in the land of Israel: ‘Time goes by, and no vision comes true’?
23 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
So tell them that this is what the Lord God says: ‘I will put a stop to this proverb. No one in Israel will quote it anymore.’ Instead tell them: The time is soon coming when every vision will come true.
24 Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
There won't be any more false visions or fake prophecies among the Israelites,
25 Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
because I, the Lord, will say whatever I choose to say, and it will happen immediately. Right now, you rebellious people, I will say something and make sure it happens, declares the Lord God.”
26 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
An additional message from the Lord came to me, saying,
27 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
“Son of man, notice what the people of Israel are saying, ‘The vision that he's describing won't happen for a long time. He's prophesying about a time in the distant future.’
28 “Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
So tell them that this is what the Lord God says: Everything I've said is about to happen. There won't be any more delay, declares the Lord God.”