< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Тада ме подиже дух, и однесе ме на источна врата дома Господњег, која гледају на исток, и гле, на вратима беше двадесет и пет људи, и међу њима видех Језанију, сина Азуровог и Фелатију сина Венајиног, поглаваре народне.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
И рече ми: Сине човечји, ови људи смишљају безакоње, и зло саветују у том граду,
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
Говорећи: Није близу; да градимо куће; овај је град лонац а ми месо.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
Зато пророкуј против њих, пророкуј, сине човечји.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
И паде на ме дух Господњи и рече ми: Реци: Овако вели Господ: Доме Израиљев, тако говористе, и знам мисли срца вашег.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Многе побисте у том граду, и напунисте улице њихове побијених.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
Зато овако вели Господ Господ: Које побисте и побацасте усред њега, они су месо, а он је лонац, а вас ћу извести из њега.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Бојите се мача; мач ћу пустити на вас, говори Господ Господ.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
И извешћу вас из њега, и даћу вас у руке туђинцима, и извршићу на вама судове.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Од мача ћете пасти, на међи Израиљевој судићу вам, и познаћете да сам ја Господ.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
Овај град неће вам бити лонац нити ћете ви бити у њему месо; на међи Израиљевој судићу вам.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
И познаћете да сам ја Господ, јер по уредбама мојим не ходисте нити законе моје извршавасте, него чинисте по законима тих народа што су око вас.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
А кад пророковах, умре Фелатија син Венајин; тада падох на лице своје и повиках гласно и рекох: Јаох Господе Господе! Хоћеш ли да истребиш остатак Израиљев?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
А глас Господњи дође ми говорећи:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Сине човечји, браћа су твоја, браћа твоја, родбина твоја и дом Израиљев васколики, којима говорише Јерусалимљани: Идите далеко од Господа, нама је дата земља у наследство.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
Зато реци: Овако вели Господ Господ: Ако их и одагнах далеко међу народе, ако их и расејах по земљама, опет ћу им бити светиња за мало у земљама у које отидоше.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
Зато реци: Овако вели Господ Господ: Сабраћу вас из народа и покупићу вас из земаља у које се расејасте, и даћу вам земљу Израиљеву.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
И кад дођу у њу, избациће из ње све гадове њене и све гнусобе њене.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
И даћу им једно срце, и нов дух метнућу у њих, и извадићу из тела њиховог камено срце и даћу им срце месно,
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
Да би ходили по мојим уредбама и држали моје законе и извршавали их; и биће ми народ, и ја ћу им бити Бог.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
А којима срце иде по жељи гнусоба њихових и гадова њихових, њихов ћу пут обратити на њихову главу, говори Господ Господ.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Потом махнуше херувими крилима својим, и точкови отидоше према њима, и слава Бога Израиљевог беше озго над њима.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
И подиже се слава Господња исред града, и стаде на гори која је с истока граду.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
А мене дух подиже и однесе у утвари духом Божјим у Халдејску к робљу: и утвара коју видех отиде од мене.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
И казах робљу све речи Господње што ми показа.

< Ezekiyel 11 >