< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Além disso, o Espírito me levantou e me levou ao portão leste da casa de Yahweh, que olha para o leste. Eis que vinte e cinco homens estavam à porta do portão; e vi entre eles Jaazanias, filho de Azzur, e Pelatiah, filho de Benaías, príncipes do povo.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
Ele me disse: “Filho do homem, estes são os homens que planejam a iniqüidade, e que dão conselhos perversos nesta cidade;
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
que dizem: 'O tempo não está próximo de construir casas'. Este é o caldeirão, e nós somos a carne”.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
Portanto, profetiza contra eles. Profetiza, filho do homem”.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
O Espírito de Javé caiu sobre mim, e ele me disse: “Fala, 'Javé diz: “Assim disseste tu, casa de Israel; pois eu sei as coisas que te vêm à mente.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Vocês multiplicaram seus mortos nesta cidade, e encheram suas ruas com os mortos”.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
“'Portanto o Senhor Javé diz: “Seus mortos que você colocou no meio dela, eles são a carne, e este é o caldeirão; mas você será trazido para fora do meio dela.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Temestes a espada; e eu trarei a espada sobre vós”, diz o Senhor Yahweh.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
“Eu vos tirarei do meio dela, e vos entregarei nas mãos de estranhos, e executarei julgamentos entre vós”.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Você cairá pela espada. Julgar-vos-ei na fronteira de Israel”. Então você saberá que eu sou Yahweh.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
Este não será seu caldeirão, nem você será a carne no meio dele. Eu o julgarei na fronteira de Israel.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
Você saberá que eu sou Iavé, pois você não andou nos meus estatutos. Vocês não executaram minhas ordenanças, mas o fizeram após as ordenanças das nações que estão ao seu redor””.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
Quando profetizei, Pelatiah, o filho de Benaiah, morreu. Então eu caí de cara, chorei em voz alta e disse: “Ah Senhor Yahweh! Vós fareis um fim completo do remanescente de Israel”?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A palavra de Javé veio a mim, dizendo:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
“Filho do homem, seus irmãos, até mesmo seus irmãos, os homens de seus parentes, e toda a casa de Israel, todos eles, são aqueles a quem os habitantes de Jerusalém disseram: 'Vá para longe de Javé'. Esta terra nos foi dada por uma possessão”.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
“Portanto, diz: 'O Senhor Javé diz: “Enquanto eu os afastei para longe entre as nações, e enquanto os espalhei entre os países, ainda assim serei para eles um santuário por algum tempo nos países onde eles vieram””.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
“Portanto, diz o Senhor Javé: “Eu vos congregarei dos povos e vos congregarei fora dos países onde fostes espalhados, e vos darei a terra de Israel”.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
“'Eles virão para lá e tirarão de lá todas as suas coisas detestáveis e todas as suas abominações.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
Eu lhes darei um coração, e colocarei um novo espírito dentro deles. Tirarei o coração pedregoso de sua carne e lhes darei um coração de carne,
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
para que possam caminhar em meus estatutos, e manter minhas ordenanças, e as façam. Eles serão meu povo, e eu serei seu Deus.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Mas quanto àqueles cujo coração anda atrás do coração de suas coisas detestáveis e de suas abominações, eu lhes trarei o caminho sobre suas próprias cabeças', diz o Senhor Javé”.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Então os querubins levantaram suas asas, e as rodas estavam ao lado deles. A glória do Deus de Israel estava sobre eles acima.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
A glória de Yahweh subiu do meio da cidade, e ficou na montanha que fica no lado leste da cidade.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
O Espírito me levantou, e me trouxe na visão pelo Espírito de Deus para a Caldéia, para os cativos. Então a visão que eu tinha visto subiu de mim.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
Depois falei com os cativos todas as coisas que Yahweh tinha me mostrado.

< Ezekiyel 11 >